< Ndu Manzaniba 14 >

1 Aye he toki ni Iconium, wa Bulus mba Barnaba ba ri hi nimi Synagogue wu bi Yahudawa ba, nda ka tre hu ninkon wa kpaandi, ba Yahudawa baba Greeks ba kpanyeme.
A Ikoniyum Bulus da Barnabas suka shiga majami’ar Yahudawa yadda suka saba. A can suka yi magana gabagadi har Yahudawa da Al’ummai masu yawa suka gaskata.
2 Ama Yahudawa wa ba kamba ni zren huba'a, ba chon dri bi kora ba nda duba ti nfu ni mri vayi mba.
Amma Yahudawan da suka ƙi ba da gaskata, suka zuga Al’ummai suka sa ɓata tsakaninsu da’yan’uwa.
3 Nitu ki, ba ki niki gbron nton, ndani bla gbangban me ni gbengblen Bachi, ndani tsro ba du ba toh tre wa a ton ba wu ya ndindi. A ti toki niwa a tsro kpanyeme wa ndji ba toh ni kikle kpi waasi ti ni shishi mba, zu ni wo bulus mba Barnaba.
Bulus da Barnabas kuwa suka daɗe sosai a can, suna magana gabagadi saboda Ubangiji, wanda kuwa ya tabbatar da saƙon alherinsa ta wurinsa su su aikata ayyuka da alamu masu banmamaki.
4 Ama ndji bi gbu'a ba gaanyu, bari ba kri ni ngbala Yahudawa, i bari ni manzani ba.
Mutanen birnin suka rarrabu, waɗansu suka goyi bayan Yahudawa, waɗansu kuma suka goyi bayan manzannin.
5 Wawu mba, bi kora mba Yahudawa (baba bi ninkon mba) ba wa nkon wu vu ba yo ya nda ta ba Bulus mba Barnaba ni tita,
Yahudawa da Al’ummai tare da shugabanninsu suka ƙulla shawara a tsakaninsu, domin su wulaƙanta su su kuma jajjefe su da duwatsu.
6 ama niwa ba ble wo toki, ba tsutsu hi ni igbu bi Lycaonia, wu Lystra mba Derbe baba kaagon gran bi koki,
Amma suka sami labari suka kuma gudu zuwa biranen Ikoniyum na Listira da Derbe da kuma ƙauyukan kewaye,
7 niki ba si zren ni d'bu tre ndindi'a.
inda suka ci gaba da wa’azin labari mai daɗi.
8 Ni Lystra, iguri a son, hamma ni gbengblen ni zama, chon kple rhi ni nne yimma, wa ana zren to ni son ma na.
A Listira kuwa akwai wani gurgu zaune a ƙafafunsa, wanda gurgu ne tun haihuwa, kuma bai taɓa tafiya ba.
9 Iguyi a wo bulus si tre. Bulus a yo shishi ma niwu nda toh ndi a he ni sron kpanyeme nitu kpa sii kpama.
Ya kasa kunne yayinda Bulus yake magana. Bulus kuma ya kafa masa ido, ya lura cewa yana da bangaskiyar da za tă warkar da shi
10 Niki a tre niwu ni kikle lan ndi, “Lu kri ni za me.” Mleigu'a a lu za kri nda zren kaagon.
sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi ka tsaya kan ƙafafunka!” Da jin haka, sai mutumin ya yi wuf ya kuma fara tafiya.
11 Niwa kpaandi ba bato kpewa Bulus a ti'a, ba nzu lan ba ndani tre ni el'pa Lycaonia, “Ba rji ba ba k'ma rhu too ndji nda grji ye nita.”
Sa’ad da taron suka ga abin da Bulus ya yi, sai suka ihu da harshen Likayoniyawa, suna cewa, “Alloli sun sauka mana da siffar mutane!”
12 Ba yo Barnaba ndi “Zeus,” mba Bulus, “Hermes,” nitu wawuyi ana ninkon wu lantre'a.
Sai suka ba wa Barnabas, sunan Zeyus, Bulus kuma suka kira Hermes domin shi ne shugaban magana.
13 Priest wu irji zeus, wa koobre ma ahe ni kogon kikle gbu'a, anji kikle lando wa ba yra ni loh bre ye ni kikle nkontra gbu'a, wawu mba gbugbu ndji ba, nitu duba ye gon nton nibawu.
Firist na Zeyus, wanda haikalinsa ke bayan birni, ya kawo bijimai da furanni a ƙofofin birni domin shi da taron mutanen sun so su miƙa musu hadayu.
14 Niwa manzani ba, Bulus mba Barnaba ba wo toki, ba y'ba nklon mba nda tsutsu hi nda ka kuuyi ni mi ndji ba
Amma da manzannin nan Barnabas da Bulus suka ji haka, sai suka yayyage tufafinsu suka ruga cikin taron, suna ihu suna cewa,
15 nda ni hla ndi, “Indji-lon, nitu ngye bi ti kpi biyi? Kita ngame ki ndji, ni kpa too wumbi. Kisi bla tre ndindi ni yiwu nitu duyi k'ma gon don meme kpi ndi ye ni Irji wu sissren, wa a ti shulu, ni memee ni kpaama teku, mba wawu kpi wa bahe ni mi mba.
“Ya ku mutane, don me kuke yin haka? Ai, mu ma mutane ne kawai,’yan adam ne kamar ku. Mun kawo muku labari mai daɗi ne, muna gaya muku ku juya daga waɗannan abubuwa banza, ku juyo ga Allah mai rai, wanda ya yi sama da ƙasa da teku da kuma dukan abin da yake cikinsu.
16 NI k'ba wa baka hiye, a du gbungblu du ba zren ni nkon kankan wu mba.
A zamanin dā, ya bar dukan ƙasashe su yi yadda suka ga dama.
17 Ni kima me, ana hamma ni don wa ba bla kpewa ba to nituma na, niwa a ti kpiwu bi nda nuba mma-lu rhini shulu mba ntonlu wa niye nuyi klo biri bran; shuuni sron mba ni biri mba ngyiri kpukpome.
Duk da haka bai bar kansa babu shaida ba. Ya nuna alheri ta wurin ba ku ruwan sama da kuma amfanin gona a lokutansu; ya ba ku abinci mai yawa ya kuma cika zukatanku da farin ciki.”
18 Ni lantre bihi me, Bulus mba Barnaba ba mla zu ndji ba megen bubu gon nton ni bawu.
Ko da waɗannan kalmomi ma, da ƙyar suka hana jama’an nan yin musu hadaya.
19 Ama Yahudawa bari wa ba rhini Antioch mba Iconium, ba ye kma tu ndji ba sran ni gyru bre. Ba taa Bulus ni tita nda ngbiwu rju hi ni kogon gbu'a, nda ban ni mren mba ndi a qu ye.
Sai waɗansu Yahudawa suka zo daga Antiyok da Ikoniyum suka sha kan taron. Suka jajjefi Bulus da duwatsu suka kuma ja shi bayan birni, suna tsammani ya mutu.
20 Ni kime, niwa mriko ba ka kri kaagon nitu ma, alu kri nda zren ri ni mi gbu'a. Ni vi wa a hu kima, a hi ni Derbe wawu'u mba Barnaba.
Amma bayan da almajiran suka taru kewaye da shi, sai ya tashi ya koma cikin birni. Kashegari shi da Barnabas suka tashi zuwa Derbe.
21 Hu gon wa baka d'bu bla tre ndindi nitu ma, ni mi gbu'a nda mriko gbugbu, ba k'ma ye ni Lystra, ni Iconium mba ni Antioch.
Suka yi wa’azin Labari mai daɗi a wannan birni, suka kuma sami almajirai da yawa. Sai suka koma Listira, Ikoniyum da kuma Antiyok,
22 Ba si nron mriko ba duba kri ni sron gbangban nda yo ni bawu du ba na k'ma ya gon ni kpa nyme mba ndani tre ndi, “Abi toki duta ri ni ko Irji hu ni nkon iya
suna gina almajirai suna kuma ƙarfafa su su tsaya da gaske cikin bangaskiya. Suka ce, “Sai da shan wahaloli masu yawa za mu shiga mulkin Allah.”
23 Niwa ba yo bi ninkon nitu mba, ni ekklisiya ba, nda bre Irji hamma ni rhikpe, ba kaba yo ni wo Bachi wa nituma yi ba kpa nyeme.
Bulus da Barnabas suka naɗa musu dattawa a kowace ikkilisiya, tare da addu’a da azumi, suka miƙa su ga Ubangiji, wanda suka dogara da shi.
24 Mle ba zrenzu ni Pisidia nda ye ri ni Pamphylia.
Bayan sun bi ta Fisidiya, sai suka zo cikin Famfiliya,
25 Niwa ba kle bla lantre'a ni Perga, ba grji hi ni Attalia.
kuma sa’ad da suka yi wa’azi a Ferga, sai suka gangara zuwa Attaliya.
26 Rhi niki ba zren zu nitu mma ka rini Antioch, ni bubu wa bana nzuba yo ni toh ti Irji wu ndu wa baka kle'u zizan.
Daga Attaliya kuma suka shiga jirgin ruwa suka koma Antiyok, inda dā aka danƙa su ga alherin Allah saboda aikin da suka kammala yanzu.
27 Niwa ba ye ri nimi Antioch, ba yo ekklisiya zi ni bubu riri, nda vubla bawu wawu kpiwa Irji a ka ti niba, mba nitu wa a bwunko wu kpa gbangban ni biwa babi kora'a.
Da isarsu a can, sai suka tara ikkilisiya wuri ɗaya suka ba da rahoton duk abin da Allah ya aikata ta wurinsu da kuma yadda ya buɗe ƙofar bangaskiya domin Al’ummai.
28 Ba kii wu gbron nton ni ba mriko ba,
Suka kuma jima a can tare da almajirai.

< Ndu Manzaniba 14 >