< Ndu Manzaniba 12 >
1 Zizan, wieiweire ni nton wa Herod, kikle chu'a a saa wo nitu biwa ba bi ikklissiya ba, nitu du vu ba tiiya.
A lokacin nan Sarki Hiridus ya sa wa wasu masu bi hannu domin ya musguna masu.
2 A wuu Yakubu vayi Yohana ni Takobi.
Ya kashe Yakubu dan'uwan Yahaya da takobi.
3 Hu gon wa ato ndi kima a biya ni Yahudawa ba, a hon hi ka vu Bitrus ngame. Kima a he ni ba vi wu bredi wandi ba klan hamma ni du sa nda en na.
Bayan da ya ga hakan ya gamshi Yahudawa, sai ya kama Bitrus ma.
4 Niwa a vuulo'a, a njiwu ka tro ni kotro, ni wo sojoji nklan nza du ba mla ya; a ta son ndji wa ani njiwu rjuye nu ndji hu kle igan-u nigra.
Bayan ya kama shi, sai ya tsare shi a kurkuku ya kuwa sa sojoji hudu su dinga tsaron sa; yana niyyar kawo shi gaban mutanen a bayan Idin katarewa.
5 Toki, ba tro Bitrus zi ni tra tro, ama biwa ba bi ekklisiya ba kri gbangban ni bre Irji ni tu ma.
To, Bitrus na tsare a kurkuku, amma 'yan'uwa na iklisiya suna yin addu'a ga Allah sosai domin sa.
6 Nichu wa mble ka nhran hu'a, Herod anata chu rjuye duba bla tre nituma, Bitrus a sia kruna ni tsutsu sojoji harhi, nimi lo ni sraka harhi, ni bi gben ni nyu nkontra ni duba mla ta ya nkontra'a.
Ana kamar gobe Hiridus zai fitar da shi, a wannan daren, Bitrus yana barci a tsakanin sojoji biyu, daure da sarkoki biyu; sojoji kuma na gadi a bakin kurkukun.
7 Mle, Maleka Bachi a lu kri tanwrhu, ikpan lu ri nda kri bwu tra wu ko tro'a, ndu ku wrhu Bitrus ni kosan nda ta'u sh'me ni nna'a nda hlawu ndi, “Lukri gbagbla,” u sraka'a ba ju kuhle rjini woma.
Ba zato, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gareshi, haske ya haskaka dakin. Ya taba Bitrus a gefe ya tashe shi kuma ya ce, “Tashi da sauri.” Sai ga sarkokin suka zube daga hannunsa.
8 Maleka a hlawu ndi, “Lo kpame ni vu lagban wu zame sru.” Bitrus a tie toki. Maleka a hlawu ndi “Vu nklon me wu kora'a sru ni hume.”
Mala'ikan ya ce masa, “Yi damara ka sa takalmanka.” Bitrus kuwa yayi haka. Mala'ikan ce ma sa, “Yafa mayafinka, ka biyo ni.”
9 Niki, Bitrus a hu Maleka zren rju. Ana to ndi kpe wa Maleka a tia a hi njanji na. A tre ndi a si toh ni raa mu.
Bitrus kuwa ya bi mala'ikan suka fita waje. Bai gane abin da mala'ikan ke yi zahiri ne ba. Yana zaton ko yana ganin wahayi ne.
10 Niwa ba zren ka vu y'ba bi gben bi mumla, mba wu ha, nda ye ni kikle nkon karfe wu ri ni gbu'a, a bwu kikima ni bawu. Ba rju grji hu nkon wu mi gbu'a, u Maleka a kri kaado.
Bayan da suka wuce masu tsaron fari da na biyu, sun kai kofar da aka yi da karfe wadda ta mike zuwa cikin gari; ta bude masu da kanta. Suka fita sun bi titin, kuma nan take kuma sai mala'ikan ya bar shi.
11 Niwa mren Bitrus a k'ma ye niwu, a tre ndi, “Zizan, mi mla toh wu njanji ndi Bachi yi a ton Maleka ni du ye kpame chuwo ni wo Hiridus, mba wawu kpi wa Yahudawa ba bata yo shishi ndi ba toh.”
Da Bitrus ya komo hayyacin sa, ya ce, “Hakika yanzu na gane Ubangiji ya aiko da mala'ikansa don ya kubutar da ni daga hannun Hiridus da abin da Yahudawa suke zato.”
12 Ni mla to toki, a zren hi ni ko Maryamu iyi Yohana, wa ba yo ndi Markus ngame, niki ndji gbugbuwu bana zontu ki si bre Irji.
Da ya gane haka, ya zo gidan Maryamu mahaifiyar Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus; masu bi da yawa sun taru a can suna addu'a.
13 Niwa a wrunkon wu kikle nkotra u ri ni ko'a, vivren wa wu ndu ni ko'a, wa ndema hi Ruda a ye nitu du ye kpa yo'a.
Da ya kwankwasa kofar gidan, sai baiwar gidan mai suna Roda ta zo don ta bude kofar.
14 Niwa a wo lan Bitrus nda to ndi a yi wawuyi, nitu ngyiri ana bwu nkon a na nda tsutsu ri hi nimi ko'a, nda ka hla bawu ndi Bitrus kri ni nyu nkontra wu kora.
Da ta gane muryar Bitrus, don farin ciki ta kasa bude kofar; maimakon haka, ta koma daki a guje, don ta basu labari Bitrus na tsaye a bakin kofa.
15 Ba kri hlawu ndi, “Wu sran.” Ama a kri gbangban nitu a hi njanji. Ba tre ndi, “A hi ibrji ma.
Suka ce mata, “Kin haukace.” Amma ta nace da cewa haka ne. Suka ce, “Mala'ikansa ne.”
16 Ama Bitrus ana donme ni wrunko'a na, ni bwu nko mba, ba too nda kri bwunyu yo ni h'yo.
Amma Bitrus ya ci gaba da kwankwasawa, da suka bude kofar, sai suka ga ai shine, suka sha mamaki kwarai.
17 Bitrus a ti ba niwo duba son gbangbi, nda bla bawu nitu wa Bachi a njiwu rju ni kotro. A tre ndi, ton ba hi ni Yakubu baba mbru mri vayi ba nitu kpeyi. Mle a lu don ba nda zren hi ni buburi nkan.
Bitrus kuwa ya yi masu hannu yana, masu alama su yi shuru. Sai ya gaya masu labarin yadda Ubangiji ya kubutar da shi daga kurkukun. Ya ce, “Ku gaya wa Yakubu da dukan 'yan'uwa abin da ya faru.” Sai ya bar su, ya tafi wani wuri.
18 Niwa mble a nhra, ana tsitu fime wa a ri ni mi sojoji ba na nitu ka ahi ngye ti Bitrus.
Sa'anda gari ya waye ba karamar hargowa ce ta tashi a cikin sojojin ba, game da abin da ya faru da Bitrus.
19 Hu wa Hiridus a wa nda na too na, a mye bi gben ba nda yo ba ni duba wu ba. Hu ki, a grji rji ni Judiya hi ni Caesarea nda ka son niki.
Bayan da Hiridus ya neme shi kuma bai same shi ba, sai ya tambayi masu tsaron kuma ya bada umarni a kashe su. Sai ya gangara daga Yahudiya zuwa Kaisariya ya yi zamansa a can.
20 Zizan Hiridus a shu ni nfu ni ndji bi Tyre mba Sidon. Ba hi niwu nitu kpe riri, nda weire Blastus, wa ani zo ninkon chu'a ndu, andi du yo nyu zoba, ba mye ndi duba ki ni sikpe ni gbungblu meme wu nikon chu'a.
Yanzu kuwa Hiridus ya yi fushi sosai da mutanen Taya da Sidon. Suka tafi wurinsa tare. Suka roki Bilastasa, mataimakin sarkin, ya taimake su. Sai suka nemi sasantawa don suna samun abinci daga kasarsa ne.
21 Ni vi wa ba yo'a, Hiridus a sru nklon ma u bi chu nda son ni ruron wu tu chuma, nda lu tre ni ba.
A ranan da aka kayyade, Hirudus ya sha damara da kayan saurata kuma ya zauna akan kursiyi; ya yi masu jawabi.
22 Ndji ba ba kpagro ndi, “Wayi hi lan Irji ana wu ndji na!”
Mutanen suka yi ihu, “Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!”
23 Hari me, Maleka Bachi a kri yo wru, nitu ana nu Irji ninkon na; ntson mra ba kri rhiwu wuu.
Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.
24 Ama lantre Irji a si bwu bran ndani krigbu.
Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya.
25 Niki, niwa Barnabas mba Shawulu ba kle ndu zren mba, ba k'ma zren rji ni Urishelima, nda nji nha niba Yohana, wa ba yo ndi Markus
Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne. [Barnaba da Shawulu suka koma Urushalima.]