< Ndu Manzaniba 1 >

1 Ikpi biwa mina hla niwu'a, Theophilus, a ne nitu ndu u tsro wa Yesu a ti rhi ni mumla.
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 Ahe ni iri wa ba bariu hi ni shu, nikima wa a 'mmha manzani wa ana chuba'a ni ruhu tsatsra, a.
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 Niwa baya wa ba tiu ya a stro tuma ni sisren ni bawu ni nkon kankan ni du ba na kpatron ni lunde ni be mana A tsro tuma nibawu wu vi tsotra don za nda tre ni ba nitu koson (shulu) Irjhi.
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 Niwa a kri ni shubimba ni wu, a'mmha ba du bana don Urishilima na, du ba gben shirjhi wu tima, wa a lha ndi, “Bi wo ni nyumu.
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 Ndi a hi janji, Yohanna a ti batisma ni yiwu ni ma, ama ni vi yi, bi kpa batisma wu Ruhu Tsatsra.”
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 Niwa ba shu ki, ba miye ndi baci, “zizanyi ahi ton yiyi u kma tuchu gbungblua ye ni Israila?
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 A lha bawu ndi “Ana wumbi du yi to nton ko vi waa timu a yo ni gbengble ma na.”
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8 Ama bi kpa gbengble wa Ruhu Tsatsra ni ku yiwu, niki bi bla ni tumu, rhi ni Urishilima baba Judiya wawu mba Samaria, ni ka ri ni klekle gbungblu meme.
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 A kle tre kpi bi yi nu, niwa ba ki si ya shulu, ba ban'u lu hon, e clalu a kawu u shishi mba ka la tou na.
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 Niwa ba rhisi yo shishi ni ya hon ma hi shulu'a, ndhi ha ni nkon kinkla ba krirhu kri ni mimba.
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 Ba tre ndi, “Biyi ndhi bi Galilee, “bi ki ya gye ni shulu? Yesu yi, wa ba banwu hi ni shulu, ni kima ye bibi wa bito ba ban u hi ni shulu'a”
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Mle ba k'ma grhi rhi ni ngblu wa ba yo ndi Olivet, wandi a wiewiera ni Urishilima, hi ni mi gbu Urishislima, ezren vi chanchu sati.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 Niwa ba ye ri, ba tsi hunhi tra u koshu, wa bah kini mia. Bana ba Yohana, yakubu, andarawus, Filibus, Toma, barthelomen, Matiu, Yakubu Ivren Alphanso Siman wa ini wu ngyegere me, Mba Juda Ivren Yakubu.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 Wawu mba ba zontu ki ni bubu riri nda sia bre Rji, baba Mba ba, ni Maryamu ehi Yesu, baba mri vayi ma.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 Niri baki, Bitrus a lu kri ni mi mri vayiba, bana tsra ndhi 120, nda tre ndi.
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 “Mri vayi, a he nitu du tre wu vunvu tre baci du rhu tsra, nawa Ruhu Tsatsra ana lha ni nyu Dawuda ni tu Juda, wa a tsro biwa baye vu Yesu nkon.
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 Ana irimbu wa a kpa ndu wandi anuta ngame.”
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 (Zizan ndhi yi a ka le irhu ni nkle wu meme dri wandi a kpa'a, nda ka rhoku nitu u Kpama ka yrahle, ni irhenma ba ka vrale ni meme.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 Wawu ndhi bi ki ni gbu Urishilima ba wo kpe wa a zren kima ba yonde irhu kima ni lan gbu mba ndi. “Akeldama”, wandi a tsra ni nde “Irhu u yi.”)
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 Ba tre ni tuma ni vunvu tre zabura, ndi, “Du ba du irhukima du kri ton kpo, e du ko ndior na kruko ni kimana
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 Ani bi du lilon ri wa azi wuta rhini nton wa baci Yesu a zren ri nda rhu ni mi mbu,
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 Rjhini baptisma wu Yohana, ye ni vi wa ba ban'wu hon ni shishi mbu, nda toh tash'men rhi ni qu ngame.
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 Ba ju nji ha zi, Yusufu wandi ba yondi Barsabbas, wandi bata yondi Justus ngame, mba Matayas.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 Ba bre ndi “Baci, wuhi wu toh suron ndhi ko nha, tsro ta ka ahi nya nimi ndi bihi wa wu chu
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
25 ni du ban bubu son manzani wu bla kpe wa ato, nitu tash'm ma ni mimbu, wandi Juda a k'ma gon tiwu nda hi kpama.”
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 Ba yo kuriya nitu mba, wa a ku nitu Matayas, e ba bla a yo ni manzani wlo don iri ba.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.

< Ndu Manzaniba 1 >