< Matiwos Dooshishiyo 27 >
1 Guur datsgatson kahni naashwotsnat dats eenash jametswots Iyesus ats b́k'iritwok'o angshosh boshiyeyi.
Da gari ya waye, duk manyan firistoci da dattawan jama'a suka shirya yadda zasu kulla makirci domin su kashe shi.
2 Maniyak Iyesusi tipdek' amt dats k'eezirwo P'ilat'ossh beshidek't boími.
Suka daure shi, suka mika shi ga gwamna Bilatus.
3 Iyesusats angshetsok'o b́ bek'tsok'on bín beshi dek't imtso Yhud b́goyni, shaash t'agoronowere kahni naashwotsnat eenashwotssh hank'o ett aani b́k'ri,
Sa'adda Yahuza, wanda ya bashe shi, ya ga an zartarwa Yesu hukuncin kisa, ya nemi tuba ya kuma mayar da azurfar talatin ga manyan firistocin da dattawan,
4 «Ash s'ayino k'irosh beshidek'at t imtsotse morro finere.» Boomó «Eshe noon eege giri! man n took kis'e!» boet.
yace, “Na yi zunubi ta wurin cin amanar mara laifi.” Amma sukace, “Ina ruwan mu? Ka ji da shi da kanka?”
5 Bíwere shaash t'agarman Ik' moots bad'ik'rat, bowoke k'az b́keshi, amtnwe guuk'at k'ir b́úwts.
Sai ya jefar da kwandalolin azurfar a kasa cikin haikalin ya kuma bar su, ya tafi ya rataye kansa.
6 Kahani naashwotswere shaash t'agar man k'aaúdek't «Ambaran s'atsi giz b́wottsotse Ik' mootse ko'íyeyiru gizots eeko nemon baziyeke» boet.
Sai babban firist ya dauki kwandalolin azurfar ya ce, “Ba daidai bane bisa ga shari'a musa wannan cikin ma'aji, saboda kudin jini ne.”
7 Mansh bo shiyeyakon ibwotsi dukosh b́ wotisha ett shal wozirwooke datso bokeewi.
Sai suka tattauna al'amarin a tsakanin su, kudin kuma suka sayi filin maginin tukwane domin makabatar baki.
8 Manatse tuutson datsman andish bodt «S'ats datsa» ett b́s'egeyiri.
Dalilin wannan ne ake kiran wurin, “Filin jini” har yau.
9 Han jangatse tuutson «Esra'el nanaúwots bo k'oortsok'on bísh wotitwo shaash t'agaro bodek',
Sai abin da aka fada ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa, “Suka dauki tsabar azurfa talatin na farashin da mutanen Isra'ila suka sa a kansa,
10 Doonzonwe taan bíazaztsok'on shal wozet datsi k'awntso dashbok'ri» ett nebiyo Ermiyas bek'on b́keewtso b́s'eeni.
suka bayar domin sayen filin mai tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”
11 Manoor Iyesus dats k'eeziru P'ilat'os shinats b́t'iini, dats k'ezirwonwere «Nee ayhudiyots naasho neeneya?» Ett bíaati, Iyesuswere «Nee ni'ettsok'oyiye» ett bí aani.
Sai Yesu ya tsaya a gaban gwamna, gwamna ya kuma tambaye shi, “Kai sarkin Yahudawa ne?” Yesu ya amsa, “Haka ka fada.”
12 Ernmó kahni naashwotsnat eenashwotsn bín s'amiyosh bo etor eegor aaniratse.
Amma da manyan firistocin da dattawan suka zarge shi, bai ce komai ba.
13 Maniyak P'ilat'os «Ay keewon neen bos'amirúwan shiyatsneya?» bí eti.
Sai Bilatus yace masa, “Baka ji dukan zarge-zargen da ake yi maka ba?”
14 Iyesusmó dats k'eezirwo ayidek't bí adfetsosh bín bos'aamiru keewosh eegoru aaniratse.
Amma bai ce masa ko kalma guda ba, sai gwamna yayi matukar mamaki.
15 Dats k'eezirwo woriwot woriwoton ayhudiyots fazigi worwot baloyon tipetswotsitse noosh bishowe err boaatfwotsitse iko b́shde'e faksho bo nema b́tesh.
To lokacin bikin idi, al'adar gwamna ne ya saki mutum guda wanda jama'a suka zaba.
16 Manoor «Barbani» eteets gond finon daneets tipetso fa'e b́ tesh.
A wannan lokacin suna da wani sanannen dan kurkuku mai suna Barabbas.
17 Manoor ashuwots ko'ebowtsere P'ilat'os, «Koni itsh t biitse it geyi? Berbannemó Krstosi eteyrwo Iyesusne?» ett boon bí aati.
To da suka tattaru, sai Bilatus yace masu, “Wa kuke so a sakar maku? Barabbas, ko Yesu wanda ake kira Almasihu?”
18 Hank'o b́ etts jangonwee okooron bín beshidek't boimirwok'o b́ dantsosha b́ teshi.
Saboda ya san sun kawo shi ne domin kishi.
19 Manoor P'ilat'os b́ angshi jooratse b́ befere b́ moo gen, «B́ jangosh hmbets t'ú taa gúmotse aydek'at tikic'tsotse ash s'aynmanats eegoru nk'alrawok'owa» etaat bwoshi.
Da yake zaune a kujerar shari'a, matarsa ta aika masa cewa, “Ka fita sha'anin mutumin nan marar laifi. Saboda na sha wahala sosai a yau cikin mafarki saboda shi.”
20 Manoor kahani naashwotsnat eenash eenashwotsn «Barban bishowe! Iyesus úd'ewe!» err bo aatitwok'o ashuwotssh boizi.
A lokacin nan manyan firistoci da dattawa suka rinjayi ra'ayin jama'a suce a sakar masu da Barabbas, a kashe Yesu.
21 Dats k'ezirwonu, «Gitetswotsitse aawi itsh t bitsishe itgeyri?» ett ashuwotsi b́ aati. «Bowere Berbani noosh bíshe» bo eti.
Sai gwamna ya tambayesu, “Wa kuke so a sakar maku?” Sukace, “Barabbas.”
22 P'lat'oswere «Eshe Krstosi eteetso Iyesusi aak'owe nok'aliti?» bíet. Jamwotswere «Jitewe!» ett boaani.
Bilatus yace masu, “Me zan yi da Yesu wanda ake kira Almasihu?” Sai duka suka amsa, “A gicciye shi.”
23 Dats k'ezirwonu eegishe? «Bí b́ t'afitso eebi?» bíet. Boomó «Jitewe!» ett aydek't bokuhi.
Sai yace, “Don me, wane laifi ya aikata?” Amma suka amsa da babbar murya, “A gicciye shi”
24 Hansh P'ilat'os keewan faye b́tiziti bako egoshoru b́ k'alrawok'o b́ bek'tsotse, manoor aatso de'eweetwok'o k'alt «Taa ashaan s'atsotse s'ayn taane, b́ s'atso it tokatse?» ett ashuwots shinatse b́kisho b́mashi.
Amma da Bilatus ya ga ba zai iya komai ba don hargitsi zai iya barkewa, ya dauki ruwa ya wanke hannuwansa a gaban jama'a, yace, “Ba ni da laifi ga jinin mutumin nan marar laifi. Ku yi abin da kuka ga dama.”
25 Ash jamwotswere «B́ s'atso noonat nona'ats wotowe» boet.
Duka mutanen sukace, “Bari jininsa ya kasance a kan mu da 'ya'yan mu.”
26 Manoor P'lat'os Barbani bitsdek't faksh b́k'r, Iyesusnmó b́ jot'iyakon b́ jiteyish beshidek't boosh b́ ími.
Sai ya sakar masu da Barabbas amma yayi wa Yesu bulala ya mika shi garesu domin su gicciye shi.
27 Manoor dats k'eezirwo kes'fwots Iyesusi dats k'eziruman múlo maantsan dek't boami, kes'f jamwots Iyesusi gúrdek't ko'eebowtsi.
Sai sojojin gwamna suka dauki Yesu zuwa farfajiya suka kuma tara dukan rundunar sojoji.
28 B́ tahono kishbazt tah bíro takbok'ri.
Suka yi masa tumbur sa'annan suka sa masa jar alkyabba.
29 Angitson shordek't dozets akliliya eteetso b́ tookats jip'ii bok'ri, b́ k'ani kishats gumbo detsik'rat, b́shinats tuk'mal dek't «Ayhudiyotsko nugusono! jeeno neesh wotowe!» ett bí ats nic'o bokaashi.
Sai suka yi masa rawanin kaya suka sa a kansa, suka kuma bashi sanda a hannunsa na dama. Suka rusuna a gabansa suna masa ba'a, suna cewa, “Ranka ya dade, Sarkin Yahudawa!”
30 Bos'udono bíats bos'udfera boteshi, b́ kishatsenowere gumbo k'aaúdek't b́ took tookats bojot'fera botesh.
Suka kuma tofa masa yawu, suka kwace sandar suka buga masa a ka.
31 Bíats tirgic'o bo kaashiyakono tah biro kishbazt b́took taho takdek't, jitosh dek't bo ami.
Bayan sun gama masa ba'a, suka cire masa alkyabbar suka sa masa kayansa, suka jagorance shi zuwa wurin da za a gicciye shi.
32 Dats keewirwo múúlotse keshoke bobefere Simoni eteefo K'erena eteets dats asho daatsdek't Iyesus mask'aliyo shefdek't b́kuritwok'o bowshi.
Da suka fito waje, sai suka iske wani Bakurame mai suna Saminu, wanda suka tilasta ya tafi tare dasu domin ya dauki gicciyen.
33 Maniyere il b́bitsonwere «Took k'oola» eteef beyokok bobodi.
Suka iso wani wuri da ake kira Golgotta, wanda ke nufin,”Wurin kwalluwa.”
34 Maniyeokon úmonton eekets weyni biro b́ úshetwok'o Iyesussh t'ints bok'ri, ernmó bí fadbek't úsho geeratse b́tesh.
Suka bashi ruwan inabi da aka gauraya da wani abu mai daci. Amma da ya 'dan-'dana shi sai ya ki sha.
35 Iyesusi bojitiyakon b́ tahats it'o shap't kaybodek'i.
Bayan da suka gicciye shi, suka kada kuri'a a kan rigarsa.
36 Manoknowere bedek'tni bín bokotfere botesh.
Suka kuma zauna suna kallonsa.
37 Bín s'amiyetsok'o kitsitwo, «Han ayhdiwots nugúso Iyesusiye?» Etirwo guut'etso b́ mask'aliy k'oyok gedbok'ri.
A sama da kansa suka sa abinda ake tuhumarsa da ita a rubuce, “Wannan shine sarkin Yahudawa.”
38 Manoor Iyesusnton git wonbedewotsi iko k'ano maants iko giro maants jit bok'ri.
An gicciye shi da 'yanfashi guda biyu, daya ta damansa dayan kuma ta hagunsa.
39 B́ ganoke beshefts teshts ashuwotswere gac'on botoko shek'efetst
Wadanda suke wucewa suna zaginsa, suna girgiza kai,
40 «Nee Ik' k'oni moo gaahr keez aawotse agetuwonoo! aab n tooko kashiwe! Ik'o naayi n wotiyal aab mask'aliyatse ood'e!» eton bíats bokashfera botesh.
suna kuma cewa, “Kai da kace zaka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku, ka ceci kanka mana! In dai kai Dan Allah ne, ka sauko daga gicciyen!”
41 Mank'o kahniy naashwots nemo danifwotsntoonat eenashwotsnton hank'o ett bíats bokaashfere botesh.
Ta haka ma manyan firistocin suka rika yi masa ba'a, tare da marubuta da shugabannin, suna cewa,
42 «K'oshwotsi kashire, b́tooknmó kashiyo falratse! bí Israe'el nugúsoni wotiyal aab mask'aliyatse ood'e, noowere bín amanone!
“Ya ceci wasu amma ya kasa ceton kansa. Shi ne sarkin Isra'ila. Ya sauko mana daga kan gicciyen, sai mu ba da gaskiya gareshi.
43 Bí Ik'ats amanere, ‹Ik'o naay taane› etre, eshe Ik'o bín shunfee wotiyal and aab bín fariwe!»
Tun da ya yarda da Allah. Bari Allahn ya cece shi mana, saboda yace, “Ni dan Allah ne.”
44 Ando mank'o bínton jitets wombediwots bín boc'ashfera botesh.
Hakan nan ma 'yanfashin guda biyu da aka gicciye su tare suka zage shi.
45 Shirt sa'aton b́tuutso jed'isa'ato b́ borfetso dats jamatse t'alu wotb́gutsi.
To tun da tsakar rana sai duhu ya rufe kasar gaba daya har karfe uku na yamma.
46 Jed'i sa'at b́ wottsok'oon Iyesus, «Elohe! elohe! lama sebek'tani?» eton k'aari eenon b́ kuhi, b́bitsonwere «T Ik'ono! t Ik'ono! eegishe taan k'aznk'ri?» eta.
Wajen karfe uku, Yesu ya tada murya mai karfi yace, “Eli, Eli lama sabaktani?” wanda ke nufin, “Allahna, Allahna, don me ka yashe ni?”
47 Manoke need'dek't teshts ashuwotsitse man shisht «Hanwo Eliyasiye b́ s'eegiri!» boet.
Da wadanda suke tsaye kusa suka ji haka, sai sukace, “Yana kiran Iliya.”
48 Manoor boyitsi iko sefnegiya eteetso dek'wat shash keewo bíts s'eentsdek't gumbats geddek't Iyesus b́úshetwok'o t'intsb́k'ri.
Nan take wani ya ruga da gudu ya dauki soso ya tsoma cikin ruwan inabi mai tsami ya soka kan sandar kara ya mika masa ya sha.
49 K'oshwotsmó «Need'owe aab́ Eliyas waar bín kashitwe wotiyal be'one!» boet.
Sai sauran sukace, “Rabu da shi mu gani ko Iliya zai zo ya cece shi.”
50 Iyesus aaniy een k'ááron kuhat b́ kasho b́ ími.
Sai Yesu ya ta da murya mai karfi yayi kuka sai ya saki ruhunsa.
51 Manoor Ik'i meyitsi magarajiwo dambe dek't dash b́ borfetso gaad'at gitoko kayb́wts, datsonwere shek'eb́wtsi, shúts s'aalwotswere kap'ebowtsi,
Sai labullen haikali ya yage gida biyu daga sama zuwa kasa. Kasa kuma ta girgiza, duwatsu suka farfashe.
52 Dowwotswere bok'eshere k'irt teshts S'ayin ash aywots k'irotse botuwi.
Kaburbura suka bude, tsarkaka kuwa wadanda suke barci da yawa suka tashi.
53 Dowootse keshtnwere Iyesus k'irotse b́ tuwiyakon S'ayn kitu Iyerusalemits bokindi, manokno ay ashuwotsats bobe'eyi.
Suka fito daga kaburbura bayan tashinsa, suka shiga birni mai tsarki suka bayyana ga mutane da yawa.
54 Balatsi naashonat bínton beyirwotsn Iyesusi kotirowots dats giwonat manoke wotts jamman bobek'tsok'on aydek't shatt «Arikon han Ik'o naayiye b́ teshi!» boet.
Da hafsan sojan da wadanda suke kallon Yesu suka ga girgizar kasar da abinda ya faru, suka ji tsoro kwarai sukace, “Hakika wannan Dan Allah ne”
55 Wokoon wotdek't man s'iliru ay máátswots manoke fa'ano botesh, boowere Geliln tuut Iyesussh finefetst b́ shutsats bosha'efera boteshi.
Mata dayawa da suka bi Yesu daga Galili domin su lura da shi suka tsaya suna kallo daga nesa.
56 Boyitsnowere megdelawiti eteetsu Mariyamna Yak'obnat Yosef ind mariymna Zebdiyos nanaúwots indna manoke fa'úwotsi.
A cikin su akwai Maryamu Magadaliya, Maryamu uwar Yesu da Yusufu, da uwar 'ya'yan Zabadi.
57 Datso b́ iliyakono Yosefi eteets asho Armatiyas eteets kitutse gaalets ash iko manok b́weyi, bíwere Iyesus danifwotsitska b́ tesh.
Da yamma sai wani attajiri mutumin Armatiya ya zo, mai suna Yusufu wanda shi ma almajirin Yesu ne.
58 Ashmanwere, P'ilat'os maantsan amt Iyesus duuno b́ k'oni, P'ilat'oswere duunman bísh imetwok'o b́azazi.
Ya je wurin Bilatus ya roka a bashi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a bashi.
59 Manoor Yosef duunman orshdekt shemi s'aynon k'odb́k'r.
Yusufu ya dauki jikin, ya rufe shi da likafani mai tsabta,
60 B́ tookish shúts s'alotse k'ewdek't b́dozts doowi handrots duukb́k'r, shúts eeno kukulshdek't doowi fengeshats is'k'rat kazbíami.
sai ya sa shi a cikin sabon kabarinsa da ya sassaka cikin dutse. Sai ya mirgina babban dutse a bakin kofar kabarin ya tafi.
61 Megdelawi dats ashu Mariyamnat k'oshu Mariyamn, manoke doowi shinatse bobefere boteshi.
Maryamu Magadaliya da dayan Maryamun suna nan zaune akasin kabarin.
62 K'andek'i aawoniyere yaatsok'o guur, kahni naashwotsnat feresawiyotsn ik wotdek' P'ilat'os maantsan amt hank'o boeti,
Washegari, wato bayan ranar Shiri, Sai manyan firistoci da Farisawa suka taru tare da Bilatus.
63 «Doonzono! dariifmań kashon befetst ‹Keez aawoniye okoon k'irotse tuwitwe› bíettso gawdek'rone.
Sukace, “Mai gida, mun tuna lokacin da mayaudarin nan yake da rai, yace, “Bayan kwana uku zan tashi.”
64 Mansh b́ danifuwots amr úmp'de ashuwotssh ‹Hamb k'irotse tuure› boerawok'o doowman keez aawo b́ borfetso kotetwok'o azazowe, man wotob́k'azal ili b́dariytwo shintsoniyere ayide gonde b́ wotiti.»
Saboda haka, ka bada umarni a tsare kabarin na kwana uku. In ba haka ba almajiransa zasu zo su sace shi, kuma su ce wa mutane, “Ya tashi daga mattatu.” Kuma yaudarar karshe zata fi ta farko muni.”
65 P'ilat'oswer «Hambe, kotet kes'fwots fa'ane, de'amr it dantsok'on kotiwere» bíet.
Bilatus yace masu, “Ku dauki masu tsaro. Kuyi tsaro iyakar karfin ku.”
66 Mansh amt shútsmanats matabon togk'rat doowman kes'fuwotsn bokoti.
Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka hatimce dutsen, suka sa masu tsaro.