< Matiwos Dooshishiyo 10 >
1 Iyesus tatse git b́ danifwotsi bíyok s'eegdek't, kim shayiro bokishitwok'o, shodonat kúúni shod jamon bokashitwok'o alo boosh b́ ími.
Yesu ya kira almajiransa goma sha biyu, ya kuma ba su ikon fitar da kazaman ruhohi, su warkar da kowacce irin cuta da rashin lafiya.
2 Tatse git wosheetsots shútsonwere hank'oyi, shin shinon P'et'rosi eteetso Sim'onnat bí eshu Indriyasi, Zebdiwos nana'uwots Yak'obnat Yohansn,
To yanzu ga sunayen manzanin nan goma sha biyu. Na farkon shine, Saminu, wanda ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, da Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya;
3 Filip'os, Bert'elemiyos, Tomasi, t'ilish dek'fo Matiwosi, Ilfyos naay Yak'ob, Tadiwos
Filibus, da Bartalamawus, da Toma da Matiyu mai karbar haraji da Yakubu dan Halfa, da Taddawus;
4 Okooretso Sim'oni, Iyesusi beshidek't imtso Keriyot asho Yihudi.
Saminu Bakairawane, da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bashe shi.
5 Iyesus tatse gitwotsi, hank'o ett boon b́woshi, «Ik' ash woterawwotsok amk'ayere, Semari dats ashuwots kitotso kindk'ayere,
Sha biyun nan su ne Yesu ya aika, ya yi masu umarni ya ce, ''Kada ku shiga wajen al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa.
6 Maniyere mereerikok'o t'afts Isra'el ashuwotsok ameree.
Sai dai ku je wurin batattun tumaki na gidan Isra'ila.
7 Amrnwere ‹Dari mengstuuniye karnraniyee!› err nabúwere.
Sa'adda kuna tafiya, kuna wa'azi, kuna cewa, 'Mulkin Sama ya kusato'.
8 Shodetswotsi kashiwere, k'irtswotsi tuuzwere, een shodetswotsi s'ayintsworee, Fo'erawwotsi kishwere, beenon it dek'tso beenon imere.
Ku warkar da marasa lafiya, ku tada matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljanu. Kyauta kuka samu ku ma ku bayar kyauta.
9 Awntso wee ambaro wee k'áázo it borsots deshdek'k'ayre.
Kada ku rike zinariya, ko azurfa, ko tagulla a jakarku.
10 Fintsosh b́ misho daatso bísh b́ geyitsotse it weerindatse k'arc'ito, git kito, gitl c'amono, gumbonowere de'amk'ayere.
Kada kuma ku dauki zabira a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci abincin sa.
11 Bíts itkindts kitotse, wee gálútse, itn dek'et asho koni b́woto t'iwintsde dande'ere, manokman fakshr it keshfetsosh bíyoke teyere.
Kowanne birni, ko kauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a cikinsa, ku kuma zauna a wurin har lokacin da za ku tashi.
12 Ash moots it kindor jamo aatwere,
In za ku shiga gida ku ce, salama a gareku.
13 Maa man it jeenosh b́wotititka wotiyal jeeno itoktso bísh boree, wotitkali wotiyalmó itoktso jeeno itsh aanowe.
Idan gidan akwai dan salama, salamarku za ta ta tabbata a gare shi. Idan kuwa babu, salamarku za ta komo maku.
14 Asho konwor itide'awo wee it aap'tso k'ebo b́ k'azetka wotiyal gal man wee kit man k'ay it keshor it tufatsi k'undo teboree.
Ga wadanda su ka ki karbar ku ko sauraron ku, idan za ku fita garin ko gidan, sai ku karkade kurar kafafunku.
15 Arikoniye itsh t keewiri, angshi aawots kit maniyere Sedomnat Gemor ashuwotsi fayet fayo ketefee.
Hakika, ina gaya maku, a ranar shari'a za a fi rangwanta wa kasar Saduma da ta Gwamrata a kan wannan birni.
16 «Hambe! mereerikok'o elahi taalotse iti twoshiri, mansh dawnzikok'o s'ekwotsi, erkndikok'o dingatwotsi wotoore.
''Duba, na aike ku kamar tumaki a tsakiyar kyarketai, don haka sai ku zama masu wayo kamar macizai, da kuma marasa barna kamar kurciyoyi.
17 Ashuwots angshosh jebats beshide itn imetune, ayhudiyots Ik' k'oni mootse iti jot'etune mansh ashuwotsatse itatso korde'ere.
Ku yi hankali da mutane, don za su kai ku gaban majalisa, su kuma yi maku bulala a majami'unsu.
18 T jangosh itn dats k'eezirwtsonat, naashwotsoko it aats angshetwok'o itin de'ameyor bonat Ik' ash woterawwots shinatse t jangosh gawitwotsi wotitute,
Za su kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda ni, domin ku bada shaida a gabansu, da kuma gaban al'ummai.
19 Mooshi jebats itn bot'intsor, it keewitwo manoori sa'atmann itsh imetwotse, ‹Aawuk'o k'alrniya, egek'una nokewiti?› err shiyanon kic'k'ayere.
Idan har sun bada ku, kada ku damu da yadda za ku yi magana, ko kuwa abin da za ku fada, domin za a ba ku abin da za ku fada a lokacin.
20 It gitsotse bede keewitwo it nih daritstso shayironi bako itnaliye.
Domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhun Ubanku ne yake magana ta bakinku.
21 Asho b́took eshwo k'irosh beshide imetwe, mank'o nihonúwere b́ took na'o k'irosh beshide imetwe, na'naonwere bo indnihwotsats balngar wotar tuwitúne, k'iroshowere boon beshide imetune.
Dan'uwa zai ba da dan'uwansa a kashe shi, uba kuwa dansa. 'Ya'ya kuma za su tayarwa iyayensu, har su sa a kashe su.
22 T jangatse ash jamoke shit'eek wotitute, ernmó b́s'uwats b́borfetso kup'de'er ned'itwo kashitwe.
Kowa kuma zai ki ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har karshe, zai tsira.
23 Kit ikutse gondbek'o itats bo ayiwor kit k'oshuts k'ay woc'ere, arikon itsh etirwe, ash na'o aanar b́waafetsosh Isra'el kit jametswotsi gúrar betsatste.
In sun tsananta maku a wannan gari, ku gudu zuwa na gaba. Hakika ina gaya maku, kafin ku gama zazzaga dukan garuruwan Isra'ila, Dan Mutum zai zo.
24 Danirwo bín danifoniyere bowatse, guutsonwere b́ doonziyere bowatse.
Almajiri ba ya fin malaminsa, bawa kuma ba yafin ubangijinsa.
25 Mansh danirwo bín danifokok'o, guutsonwere b́ doonzkok'o b́ bodal bísh bodfe. Moo doonzi ‹Beel Zebuliye› err bos'egiyakon b́ maa ashuwotsnmá maniyere bog gond shútson aawk'owe s'eego bok'azeti!
Dai dai ne almajiri ya zama kamar malaminsa, bawa kuma kamar ubangijinsa. In har sun kira mai gida Ba'alzabuba, za su kuma bata mutanen gidansa!
26 «Haniyak ashuwotsi shatk'ayere, ipetso b́ be'erawo ooritwo, ááshtsonwere b́daneraniye ooritwo eegor aaliye.
Don haka kada kuji tsoron su, domin ba abin da yake boye da ba za a bayyana ba.
27 Eshe taa t'alwotse itsh tkeewirwo, it sháánatse keewwere, shashikon it shishtso dambaan tuuts beyok waaŕ sháánatse daniwere.
Abin da nake fada maku a asirce, ku fada a sarari. Abin da kuma kuka ji a cikin rada, ku yi shelarsa daga kan soraye.
28 Meets úd'oniyere beshar kash úd'o falraw ashuwotsi shatk'ayere, maniyere kashonat meetson gahanem tawots juwo falitu Ik'o sharere. (Geenna )
Kada ku ji tsoron masu kisan jikin mutum, amma ba sa iya kashe rai. Sai dai ku ji tsoron wannan da yake da ikon kashe jiki ya kuma jefa rai cikin jahannama. (Geenna )
29 Dimbiti gitwots santim múk'wotsn kemefoshná? Wotowa eree, daritstso it nih bí eekerawon, dimbiti ikú datsatse fed'arr ooreratsanee.
Ba 'yan tsuntsaye biyu ake sayarwa akan kobo ba? Ba ko daya a cikin su da zai fadi kasa ba tare da yardar Ubanku ba.
30 It konmo dab it took s'ironwor taawekee.
Ai, ko da gashin kan ku ma duk a kidaye yake.
31 Eshe it dimbiti aywotsiyere bogts k'awntsetswotsi itwottsotse b́ jamon shatk'ayere.
Kada ku ji tsoro. Gama darajarku ta fi ta tsuntsaye masu yawa.
32 «Ash shinatse tjangosh gaw wotitu jametswotssh, taawere darotse fa'o tnih shinatse bísh gaw wotitwe.
''Saboda haka duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, ni ma zan yi shaidar sa a gaban Ubana wanda ya ke cikin Sama.
33 Ash shinatse taan haalitu jamwotsi taawere darotstso tnih shinatse haalitwee.
Amma duk wanda ya yi musun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi musun sanin sa a gaban Ubana da yake cikin Sama.''
34 «Taa twaa, jeeno datsats doosh ark'aye itsha, taa kes'a bako jeeno dek'waratsee.
''Kada ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. Ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi.
35 Taa twaa, nungush na'o b́ nihats, mááts na'ú bi indats, naayo máátsu bi awats, k'alewo tuzishee.
Domin na zo ne in hada mutum da ubansa gaba, 'ya da uwatarta, mata da kuma surukarta.
36 Mansh ashosh balangarwots b́ took maa ashuwotsiye bowotiti.
Zai zama na kuma magabtan mutum su ne mutanen gidansa.
37 Taayere bogo b́ indi wee b́nihi shunetwo, tik wotosh falratse, taayere bogo b́ nungush na'onat b́ máátsna'ú shunetwo tik woto falratse.
Dukan wanda ya fi son mahaifinsa ko mahaifayarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. Wanda kuma ya fi son dansa ko 'yarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba.
38 B́ took mask'aliyo kurde tshuutso sha'erawo asho tik woto falratse.
Wanda kuma bai dauki gicciyensa ya biyo ni ba, bai cancanci zama nawa ba.
39 B́ kashu kashiyosh geyiru jamo bin t'afitwe, b́ kashu t jangosh t'afitu jamonmó bin kashitwe.
Dukan mai son ya ceci ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, yana ceton sa ne.
40 Itn dek'etwo taan deketwe, taano dek'etwo taan woshtso Aabi dek'etwe.
''Wanda ya marabce ku, ya marabce ni ke nan.
41 Nebiyiyo nebiyi shútson dek'etwo nebiyi k'awntso daatsitwe, kááwo kááwi shútson dek'etwo kááwi k'awntso daatsitwe.
Wanda ya marabce ni kuwa, ya marabci wanda ya aiko ni. Wanda ya marabci annabi domin shi annabi ne, zai karbi lada kamar na annabi. Wanda kuma ya marabci mai adalci saboda shi mai adalci ne, zai sami lada kamar na mai adalci.
42 Arikoniye itsh tietiri, t danif b́wottsatse tuutson, múk'anotsitse ikosh aats ak'o ik brc'k'o dab imetu asho b́ k'awntso t'ud'atsee.»
Kowa ya ba daya daga cikin 'yan kananan nan, ko da kofin ruwan sanyi ya sha, domin shi almajirina ne, hakika, Ina gaya maku, ba zai rasa ladarsa ba.''