< Yoube 22 >

1 Ilaifa: se da amane sia: i,
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “Dunu afae da Gode fidimu hamedei. Dafawane! Baligili bagade dawa: su dunu amolawane da Gode fidimu hame dawa:
“Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
3 Di da moloidafa hou hamobeba: le, Gode fidimu dawa: bela: ? Hame mabu!
Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
4 Gode da dima gagabole sia: sa amola dima fofada: sa. Be amo ea bai da di da Godema nodone beda: iba: le hame.
“Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
5 Hame mabu! Dima fofada: su ea bai da di wadela: i hou hamonanebe amoga hamosa.
Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
6 Di da dia sama dima ea imunu muni ima: ne sesemusa: , ea abula huluane samogei. Amalalu, e da abula ga: simu hame ba: i.
Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
7 Di da helebe dunuma hano hame dili i. Amola ha: aligi dunuma ha: i manu imunu higa: i.
Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
8 Di da gasa bagade amola mimogo hamoiba: le, soge huluane sasamogei.
Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
9 Di da didalo uda ili fidimu higa: i. Amola di da guluba: mano ilia liligi wamolai amola ilima se iasu.
Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
10 Amaiba: le, di sa: ima: ne dogoi da di sisiga: i diala. Amola di da hedolowane beda: sa.
Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
11 Gasi da bagadeba: le, di da ba: mu gogolei. Amola hano da heda: iba: le, di hahani ba: sa.
An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
12 Gode da gadodafa Hebene ganodini esala. Amola gasumuni da gadodafa, be Gode da amo dabuagadonini ba: le gudusa.
“Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
13 Be di da amane sia: sa, ‘Gode da adi dawa: bela: ? E da mu mobiga uligi. E da habodane ninima fofada: ma: bela: ?’
Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
14 E da mu da: iya gado ahoasea, E da mu mobiga uligiba: le, nini hame ba: ma: bela: ? E da ba: mu!
Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
15 Di da wadela: i hamosu dunu ilia eso huluane ahoasu logo amoga hanabela: ?
Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
16 Ilia wadela: mu ilegei eso da mae doaga: iwane, ilia da hano leda: i amoga mini asi dagoi ba: i.
An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
17 Amo dunu ilia da Gode higasu. Ilia da Gode da ili fidimu defele esala amo dafawaneyale hame dawa: su.
Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
18 Be Gode Hi fawane da ili bagade gagui ilima i. Na da wadela: le hamosu dunu ilia asigi dawa: su hamedafa dawa: digisa.
Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
19 Gode da wadela: i hou hamosu dunu ilima se dabe iasea, noga: i dunu amola moloidafa hamosu dunu da hahawaneba: le oufesega: sa.
“Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
20 Wadela: i dunu ilia gagui liligi huluane da wadela: lesisa. Amola hame wadela: lesi liligi dialebe, amo huluane da laluga ulagisisa.
‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
21 Yoube! Di Godema olofole gousa: ma! Ema ha lasu agoane mae hamoma! Agoane hamosea, E da dima hahawane dogolegele fidisu imunu.
“Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
22 Ea dima olelebe amo lalegaguma! Ea sia: dia dogo ganodini dialoma: ne ligisima.
Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
23 Dafawane! Di fonoboiwane, Godema sinidigima! Wadela: i hou amo da dia diasuga hamonanebe ba: sa, amo huluane yolesima!
In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
24 Dia gouli huluane galadigima! Dia gouli noga: idafa amo hafoga: i hano logoa amogai sanasima!
Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
25 Gode Bagadedafa, E fawane da dia gouli amola silifa lelegela heda: i agoane dialoma: ne, logo doasima!
sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
26 Amasea, di da eso huluane Gode dafawaneyale dawa: mu. Amola E da dia hahawane hou ea bai dialebe, di da ba: mu.
Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
27 Di da Ema sia: ne gadosea, E da dima dabe adole imunu. Amola di da ilegele sia: sea, di da amo defele hamomu.
Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
28 Dia da, dia hamomu liligi huluane didili hamomu. Amola hadigi da dia ahoabe logo olemu.
Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
29 Gode da gasa fi gaguia gudulisisa. Amola E da asaboi dunu gaguia gadosa.
Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
30 Di da wadela: le hame hamosea, be moloidafa fawane hamosea, E da di gaga: mu.”
Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”

< Yoube 22 >