< Mui 18 >

1 A: ibalaha: me da Ma: melei soge amo sema ifa bagade lelebe sogebi esalu. Eso gia: beba: le, e da ea abula diasu logo holei gadenene filasa: i esalu. Amalalu, Hina Gode da ema doaga: i.
Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
2 A: ibalaha: me da ba: legadole, dunu udiana gadenene lelebe ba: i. Ba: loba, e da hedolowane ili yosia: musa: asi, amola ilima begudui.
Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
3 E amane sia: i, “Hina! Dilia da na hahawane ba: i galea, mae baligili masa.
Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
4 Na da hano gaguli misa: ne sia: mu. Amoga dilia emo dodofelalu, amo ifa ea ougiga helefima.
Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
5 Na da dilia hawa: hamosu dunu defele esala. Dilia gasa bu lama: ne, na da dilima ha: i manu imunu da defeala: ?” Ilia da bu adole i, “Defea! Dia sia: i defele hamoma!”
Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
6 Amaiba: le, A:ibalaha: me da hedolowane ea abula diasua golili sa: i. E da Selama amane sia: i, “Hedolo! Falaua 22 lida amo lale, bibiagole amola gobele agi ga: gi hamoma.”
Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
7 Amalalu, A:ibalaha: me da ea lai gebo gilisisu amoga hehenane, bulamagau mano gasono ida: iwane lale, ea hawa: hamosu dunuma i. Amo da hedolowane hahamoi.
Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
8 Amalalu, e da dodo maga: me haei, dodo maga: me amola bulamagau mano gobei, amo gaguli misini, sofe misi dunu ili amo moma: ne ligisi. Ilia da ha: i nanoba, e da ifa ea ougiga ilima gadenene lelu.
Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
9 Ilia da ema amane adole ba: i, “Dia uda Sela da habila: ?” A: ibalaha: me da bu adole i, “E da abula diasu ganodini esala.”
Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
10 Amalalu, Hina Gode da amane sia: i, “Na da waha oubi sesegeyale uduli, dafawane dima misunu. Dia uda Sela da dunu mano lalelegemu.” Sela da abula diasu holei amo Hina Gode Ea baligiga galu amoga sia: lalabolalu.
Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
11 A: ibalaha: me amola Sela da da: i hamoi dagoiba: le, Sela da mano lamu ode defei amo baligi dagoi ba: i.
Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
12 Amaiba: le, Sela da ea dogo ganodini ousu. Ea asigi dawa: su ganodini, e amane dawa: i, “Na da: i da wadela: lesi dagoi amola nagoa da da: i hamoi. Na da habodane amo hahawane hou ba: ma: bela: ?”
Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
13 Amalalu, Hina Gode da A: ibalaha: mema amane sia: i, “Sela da abuliba: le oune amane sia: i, ‘Na da da: i hamoiba: le, habodane mano lalelegema: bela: ?’
Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
14 Gasa bagade liligi hamomu da Godema hamedebela: ? Na da oubi sesegeyale uduli, eso ilegei defele na dima olelei, bu misunu. Amola Sela da dunu mano lalelegemu.”
Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
15 Sela da beda: iba: le, ogogoi. E amane sia: i, “Na da hame oui.” Be Hina Gode da amane sia: i, “Be di da oui dagoi.”
Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
16 Sofe misi dunu da masusa: wa: legadoloba, ilia da ba: le gaidi Sodame ba: i. Ilia da logoga ahoanoba, A:ibalaha: me da ili sigi asi.
Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
17 Amalalu, Hina Gode da Hima amane sia: i, “Na da waha hou hamomu amo A: ibalaha: mema wamolegema: bela: ?
Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
18 A: ibalaha: me ea fi da fi bagade amola gasa bagade hamomu. Ea houba: le, osobo bagade fifi asi gala huluane da hahawane dogolegele ilegesu ba: mu.
Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
19 Bai Na da e ilegei dagoi. E da ea mano noga: le olelema: ne amola ea fi dunu da hou moloidafa amola dafawanedafa amo olelema: ne, Na da e ilegei. Amai galea, Na da Na hahawane ilegele sia: i liligi huluane ema imunu.”
Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
20 Amalalu, Hina Gode da amane sia: i, “Na da Sodame amola Goumola ela fi wadela: idafa hou amo nabi.
Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
21 Amaiba: le, Na da ilia hou ba: ma: ne amo da nabi liligi defele ganabela: ? Amo Na da ba: la masunu. Hame galea Na da dawa: mu.”
zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
22 Sofe misi dunu da sinidigili, Sodame moilaiga doaga: musa: asi. Be A: ibalaha: me da mae fisili Hina Gode Ea midadi lelu.
Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
23 Amalalu, e da Hina Godema misini, amane sia: i, “Di da dafawane gilisili ida: iwane dunu amola wadela: i hamosu dunu ili fane legema: bela: ?
Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
24 Amabela: ? Dunu ida: iwane 50 agoane amo moilai bai bagade ganodini esalabala? Amai galea, Di da amo dunu ilia hou dawa: beba: le, amo moilai bai bagade fadegale fasima: bela: ?
Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
25 Na da agoane dawa: Di da dunu ida: iwane amola wadela: i hamosu dunu gilisili hou afadafa fawane hamomu da hamedei gala. Amo hou da Dima hame gala. Osobo bagade fifi asi gala ilima Fofada: su Dunudafa, E da hou moloidafa fawane hamoma: bela: ? Na agoane dawa: E da moloidafa hou fawane hamomu.”
Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
26 Hina Gode da bu amane sia: i, “Na da Sodame moilai bai bagade ganodini dunu ida: iwane gala 50 agoane ba: sea, Na da ilia hou dawa: beba: le, Sodame huluane hame gugunufinisimu.”
Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
27 Amalalu, A:ibalaha: me da bu sia: i, “Na da osobo amola nasubu, amo fawane. Be na da mae beda: iwane, Hina Godema sia: i dagoiba: le, na da bu sia: mu.
Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
28 Di da Sodame moilai bai bagade ganodini, dunu ida: iwane 45 fawane ba: sea, Di da 50 defei amo ganodini wadela: i hamosu dunu biyale fawane ba: sea, moilai wadela: ma: bela: ?” E bu adole i, “Na da dunu ida: iwane 45 fawane ba: sea, moilai hame gugunufinisimu.”
in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
29 A: ibalaha: me da eno amane sia: i, “Be 40 fawane ba: sea, adi hamoma: bela: ?” E amane sia: i, “Amo 40 ilia hou dawa: beba: le, Na da moilai bai bagade hame wadela: mu.”
Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
30 Amalalu, A:ibalaha: me da amane sia: i, “Hina Gode! Nama mae ougima, be na da Dima bu sia: mu. Dunu 30 fawane ida: iwane esalea adi hamoma: bela: ?” E bu adole i, “Na da 30 ba: sea, moilai hame gugunufinisimu.”
Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
31 A: ibalaha: me da amane sia: i, “Defea! Na da wali mae beda: iwane Hina Gode Ema sia: i dagoi. Be 20 fawane ba: sea?” E bu adole i, “Moloi dunu 20 ba: sea, Na da hame wadela: mu.”
Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
32 A: ibalaha: me da amane sia: i, “Hina Gode! Nama mae ougima, be na da afadafa fawane eno Dima sia: mu. Dunu 10 ida: iwane fawane ba: sea, adi hamoma: bela: ?” Hina Gode da bu adole i, “Dunu 10 ilia hou ida: iwane ba: sea, Na da amo moilai hame gugunufinisimu.”
Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
33 Hina Gode amola A: ibalaha: me, ela gilisili sia: dasu da dagoloba, Hina Gode da fisili asi amola A: ibalaha: me da hi diasuga buhagi.
Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.

< Mui 18 >