< Mousese Ea Malasu 10 >
1 Amalalu, Hina Gode da nama amane sia: i, ‘Di gele gasui aduna eno musa: hamoi defele bu hedofama. Amola ifa gagili amo gele gasui salima: ne hamoma. Amola goumiba: le heda: le Nama misa.
A lokacin Ubangiji ya ce mini, “Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka haura wurina a kan dutse. Ka kuma yi akwatin katako.
2 Amasea, Na musa: gele gasui di da goudane fasi, amoga dedei Na da dia gaheabolo hamoi gele gasuiga bu dedemu. Amasea, amo di ifa Gagili ganodini salima.
Ni kuwa zan yi rubutu a kan allunan nan biyu, kalmomin da suke a alluna na farko, waɗanda ka farfashe. Za a ajiye su a cikin akwatin.”
3 Amaiba: le, na da aga: isia ifa amoga gagili hamoi. Na da gele gasui aduna musa: liligi defele hamone, bu goumiba: le heda: le gaguli asi.
Sai na yi akwatin da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, sai na haura dutse da alluna biyun a hannuwana.
4 Amalalu, Hina Gode da Ea musa: dedei defele amo gele gasuiga bu dedei. Amo da Ea Hamoma: ne Sia: i Nabuane Gala, E da musa: dilia goumia gilisisu E da lalu amo ganodini esala dilima sia: i. E da amo gele gasui nama ianu,
Ubangiji kuwa ya sāke yin rubutu a waɗannan alluna abin da ya rubuta a allunan farko, wato, Dokoki Goma da ya furta a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar da mutane suka taru. Sai Ubangiji ya ba ni su.
5 na da sinidigili bu goumiba: le sa: i. Amalalu, Hina Gode da nama sia: i amo defele, na da amo gele gasui ifa Gagili ganodini sali. Ela da amo ganodini dialu amola wali diala.”
Sa’an nan na sauko daga dutsen, na kuma ajiye allunan a cikin akwatin da na yi, yadda Ubangiji ya umarce ni, kuma suna can a yanzu.
6 (Isala: ili dunu da Ya: ganaide gu hano yolesili Mousila moilaiga asi. Amogawi Elane da bogoi. Ilia da ea da: i hodo uli dogone, egefe Elia: isa da ea gobele salasu dunu sogebi lai.
(Isra’ilawa suka kama hanya daga rijiyoyin Beyerot Bene Ya’akan zuwa Mosera. A can Haruna ya rasu, aka kuma binne shi. Sai Eleyazar ɗansa ya gāje shi a matsayin firist.
7 Ilia da Mousila yolesili asili Gadagouda baligili Yodebada sogega doaga: i. Amogawi, ilia hano bagohame ba: i.
Daga can suka tashi zuwa Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa.
8 Amo esoha, ilia da goumia esalu, Hina Gode da Lifai fi ilia hawa: hamosu ilegei, amane, ilia da Hina Gode Ea Gousa: su Sema Gagili gaguli masunu amola Hina Gode Ea midadi leluwane hawa: hamomu, amola Ea Dioba: le, hahawane dogolegele hou olelemu. Amo hawa: hamosu ilia da wali amola hamonana.
A lokacin Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi don su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yin masa hidima, su kuma sa albarka a cikin sunansa, yadda suke yi har wa yau.
9 Isala: ili dunu huluane da soge amola liligi gagusa. Be amo defele, Lifai fi da ilisu soge o liligi o ilia ada liligi amo hame gagusa. Bai dilia Hina Gode ilima sia: i defele, ilia gagui da Hina Gode fawane.)
Shi ya sa Lawiyawa ba su da rabo, ko gādo a cikin’yan’uwansu; Ubangiji ne gādonsu yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.)
10 Mousese da eno amane sia: i, “Na musa: hamoi defele, na da goumia eso 40amola gasi 40ouesalu. Amola amo esoga, Hina Gode da na sia: nabi. E da dili gugunufinisimu hame hanai galu.
To, na kasance a kan dutse yini arba’in da dare arba’in kamar yadda dā na yi da farko. Ubangiji kuwa ya saurare ni a wannan lokaci kuma. Ba nufinsa ba ne yă hallaka ku.
11 Hina Gode da nama amane sia: i, “Masa! Na fi dunu da soge amo Na da ilia aowalali ilima imunu ilegele sia: i, ilia da amo gesowale fima: ne, di ilima bisili oule masa!”
Ubangiji ya ce mini, “Ka sauka, ka jagoranci mutanen a hanyarsu, domin su shiga, su kuma mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.”
12 Wali Isala: ili dunu fi! Nabima! Hina Gode da dilima amane sia: sa, ‘Hina Godema beda: ma amola Ema nodone sia: ne gadoma! Ea hou amoma fa: no bobogema! Dilia dogo huluane, dilia asigi dawa: su huluane amola dilia da: i hodo huluane amoga Hina Gode Ea hawa: hamosu hahawane hamoma!
Yanzu fa, ya Isra’ila, mene ne Ubangiji Allahnku yake so a gare ku, in ba ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
13 Amola Hina Gode Ea sia: amola sema dili hahawane fidima: ne, na da wali eso dilima iaha, amo huluane nabawane hamoma.
ku kuma kiyaye umarnan Ubangiji da kuma ƙa’idodinsa da nake ba ku a yau don amfaninku ba?
14 Dilia Hina Gode da mu, Hebene huluane, osobo bagade amola liligi huluane amo ganodini diala, amo E da huluane gagusa.
Sammai, har da sama sammai, da duniya, da kome da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne.
15 Be Hina Gode da dilia aowalali ilima bagadewane asigi galu. Amaiba: le, E da dunu fi eno huluane mae dawa: le, dilia aowalali iligaga fi (dilia) amo ilegei. Wali eso amo hou da diala.
Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓe ku, ku zuriyarsu, a bisa dukan al’ummai, yadda yake a yau.
16 Fedege agoane, dilia dogo gadofo damuma! Dilia gawamaga: i hou yolesima.
Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai.
17 Bai dilia Hina Gode da ‘gode’ liligi huluane baligisa amola E da ouligisu dunu huluane baligisa. E da Gode bagadedafa amola Ema beda: mu da defea. E da dunu huluane defele ba: sa. E da dunu afae baligili fidima: ne sefe hame laha amola hano hame suligisa.
Gama Ubangiji Allahnku ne Allahn alloli da Ubangijin iyayengiji, Allah mai girma, mai ƙarfi da kuma mai banrazana, wanda ba ya sonkai, ba ya cin hanci.
18 E da guluba: mano noga: le fidima: ne amola didalo huluane asigiwane fidima: ne sia: sa. E da ga fi dunu ilima asigiba: le, ema ha: i manu amola abula iaha.
Yakan tsare marayu da gwauraye, yana ƙaunar baƙon da yake zama a cikinku, yana ba su abinci da tufafi.
19 Amaiba: le, dilia amolawane ga fi dunu ilima asigima. Bai dilia musa: da ga fi dunu Idibidi soge ganodini esalu.
Sai ku ƙaunaci baƙi, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar.
20 Dilia Hina Godema beda: ma amola Ea hawa: hamosu hamoma. Dilia Gode gasa bagade lalegaguma. Dilia ilegele sia: sea, Hina Gode Ea Dioba: le sia: ma.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku kuma bauta masa. Ku manne masa, ku kuma yi rantsuwarku da sunansa.
21 E da dilia Gode, dilia nodosu liligi. E da musa: gasa bagade musa: hame ba: su hou hamoi dagoi. Amo dilia siga ba: i dagoi.
Shi ne abin yabonku; shi ne Allahnku, wanda ya aikata muku waɗancan manya abubuwa banmamaki masu banrazanar da kuka gani da idanunku.
22 70Dilia aowalalia fi da musa: Idibidi sogega gudu ahoanoba, ilia idi da70 fawane ba: i. Be wali dilia Hina Gode da hamobeba: le, dilia idi da gasumuni muagado gala amo ilia idi defele ba: sa.
Kakanninku da suka gangara zuwa Masar, su saba’in ne, yanzu kuwa Ubangiji Allahnku ya sa kuka ƙaru, kuka zama kamar taurari a sama.