< 2 Sa:miuele 10 >

1 Amogalu fa: no, A:mone soge hina bagade amo Na: iha: se da bogoi. Egefe Ha: inane da ea hina bagade sogebi lai.
Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 Hina bagade Da: ibidi da amane sia: i, “Ha: inane ea ada Na: iha: se da nama asigi galu. Amaiba: le, na da ea mano ema asigimu da defea.” Amaiba: le, Da: ibidi da sia: adola ahoasu dunu, ili da ea asigi sia: sia: ma: ne, Ha: inanema asunasi.
Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
3 Ilia A: mone sogega doaga: loba, A:mone ouligisu dunu ilia da hina bagadema amane sia: i, “Di adi dawa: bela: ? Da: ibidi da dia adama nodone dawa: beba: le, amo dunu dima asigi sia: sia: ma: ne asunasibala: ? Hame mabu! Amo da desega ahoasu dunu amo Da: ibidi da nini hasalima: ne, ninia soge hou amo hogomusa: asunasi.”
sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
4 Ha: inane da Da: ibidi ea sia: adola ahoasu dunu ili gagulaligili, ilia mayabo la: idi waga: ne, ilia abula mugagili damunisili, ili buhagima: ne asunasi.
Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
5 Ilia da buhagimu bagadewane gogosia: i. Da: ibidi da amane hamoi nababeba: le, e da ilima amane sia: si, “Dilia Yeligou moilai bai bagadega ouesalu, dilia mayabo bu sa: i galea buhagima!”
Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
6 A: mone dunu da ilia da Da: ibidi ilia ha lai hamoi dagoi dawa: i. Amaiba: le, ilia da Bedelihobe moilai amola Souba moilaiga Silia dadi gagui dunu 20,000 amola Dobe sogega dadi gagui dunu 12,000 agoane wele guda: i. Amola ilia da Ma: iga soge hina bagade amola ea dadi gagui 1,000 agoane wele guda: i.
Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
7 Da: ibidi da amo hou nababeba: le, e da Youa: be amola Isala: ili dadi gagui wa: i huluane ilima gegema: ne asunasi.
Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
8 A: mone dadi gagui dunu da gadili mogodigili, ilia da La: ba (ilia moilai bai bagade) amo ea logo holei gadenene dadalei. Silia dadi gagui dunu amola Dobe amola Ma: iaga dunu ilia da sogebi genebagela asia, amogai dadalei.
Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
9 Youa: be da ba: loba, ea ha lai da midadi amola bagia ema doagala: mu ba: i. Amaiba: le, e da Isala: ili dadi gagui dunu baligili noga: idafa amo ilegele, ilia da Silia dadi gagui dunu ilima ba: le gusuli aligima: ne asunasi.
Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
10 E da ea eya Abisia: i amo Isala: ili dadi gagui dunu eno ouligima: ne sia: i. Abisia: i da sia: beba: le, amo Isala: ili dadi gagui da A: mone dunu ilima ba: le gusuli dadalei.
Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
11 Youa: be da Abisia: i ema amane sia: i, “Di da Silia dunu na hasalimusa: heda: be ba: sea, na fidila misa. Amola na da A: mone dunu di hasalimusa: heda: be ba: sea, na da di fidila masunu.
Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
12 Di mae beda: ne gasa fima! Ninia fi dunu amola Gode Ea moilai bai bagade huluane gaga: musa: , gasa fili hamoma. Amola Hina Gode Ea hamomusa: ilegei, amo ba: mu da defea!”
Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
13 Youa: be amola ea dunu da doagala: musa: gusuba: i manebeba: le, Silia dunu ilia da hobea: i.
Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
14 A: mone dunu da Silia dunu hobealebe ba: lu, ilia da Abisia: i ema hobeale, moilai amo ganodini hehenane golili sa: i. Amalalu, Youa: be da A: mone dunuma gegenanu yolesili, Yelusaleme moilai bai bagadega buhagi.
Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
15 Silia dunu da Isala: ili dunu da ili hasali dagoi amo dawa: loba, ilia da ilia dadi gagui dunu huluanedafa gilisima: ne wele sia: i.
Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
16 Hina bagade Ha: da: disa da Silia dunu huluane amo Iufala: idisi Hano gusudili esalu, amo ema misa: ne sia: si. Ilia da Hila: me sogega misi. Sioubage (Souba hina bagade Ha: da: disa, amo ea dadi gagui wa: i ouligisudafa dunu galu) da ili ouligisu.
Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
17 Da: ibidi da amo sia: nababeba: le, e da Isala: ili dadi gagui dunu gilisili, Yodane Hano degele, Hila: me sogega mogodigili asi. Amogawi, Silia dunu da ilima ba: le gusuli dadalele, gegesu da mui.
Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
18 Isala: ili dunu da Silia dunuma gegesa fula se bobogei. Da: ibidi amola ea dunu da Silia sa: liode amoga fila heda: i dunu 700 agoane amola hosi da: iya fila heda: i dunu 40,000 agoane fane lelegei. Ilia da Sioubage (ilia ha lai ouligisudafa) amo fa: ginisili, e da gegesu sogebi amogawi bogoi.
Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
19 Hina bagade Ha: da: disa da eno hina bagade fonobahadi ouligisu. Ilia da Isala: ili dunu da ilima hasali dagoi ba: i. Amaiba: le, ilia da Isala: ili dunuma olofomusa: gousa: i. Amalalu, Isala: ili dunu da ili ouligilalu. Amola Silia dunu da beda: iba: le, bu A: mone dunu hame fidisu.
Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.

< 2 Sa:miuele 10 >