< 2 Hina 3 >

1 Yuda hina bagade Yihosiafa: de da ode18 ouligilalu, Youla: me (A: iha: be egefe) da Isala: ili hina bagade hamoi. E da Samelia moilai bai bagade amo ganodini esala, ode fagoyale agoane Isala: ili ouligi.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 E da Hina Godema wadela: le hamoi, be ea ada amola eme Yesebele, elea wadela: i hou hamoi amo defeledafa hame hamoi. E da Ba: ilema nodone sia: ne gadosu ‘gode’ agoaila, amo eda ea hamoi, amo mugululi sali.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Be amomane, hina bagade Yelouboua: me (Niba: de egefe) amo ea hou defele, e da Isala: ili fi wadela: le hamoma: ne oule asili, amola amo hou fisimusa: hame dawa: i.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Moua: be hina bagade Misia da sibi fofole ouligi. Ode huluane, e da ea lasu su dabe iasu, 100,000 sibi mano amola 100,000 sibi ilia hinabo goloi, amo Isala: ili hina bagade ema iasu.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Be Isala: ili hina bagade A: iha: be da bogobeba: le, Misia da Isala: ili fi ilima odoga: i.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Isala: ili hina bagade da hedolowane Samelia yolesili, ea dadi gagui dunu gagadoi.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 E da Yuda hina bagade Yihosiafa: dema sia: amane adosi, “Moua: be hina bagade da nama odoga: sa. Di da nama madelale ema gegema: bela: ?” Hina bagade Yihosiafa: de da amane bu adole i, “Ma! Amamuda! Na amola na dunu amola na fila heda: le gegesu hosi da dia hanai defele hamomu.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Ninia da logo habidili asili, doagala: ma: bela: ?” Youla: me da bu adole i, “Ninia da logo sedade, Idome hafoga: i sogedili masunu!”
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Amaiba: le, hina bagade Youla: me amola Yuda hina bagade amola Idome hina bagade da wa: le asi. Eso fesuale agoane mogodigili ahoanoba, hano di da ebeleiba: le, dunu amola ohe da hano manu hame ba: i.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Hina bagade Yelouboua: me da amane sia: i, “Waiye! Ninimone masunu hamedei! Hina Gode da hina bagade dunu udiana ninima, nini Moua: be hina bagade nini hasalasimusa: gegedolesibala: !”
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Hina bagade Yihosiafa: de da amane adole ba: i, “Goegai balofede dunu afae, ea da Hina Godema adole ba: mu ganabela: ?” Hina bagade Youla: me ea dadi gagui ouligisu dunu afae da amane adole i, “Ilaisia (Sia: ifa: de egefe) da goegai lela. E da Ilaidia ea afoha hawa: hamosu dunu galu.”
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Yihosiafa: de da amane sia: i, “E da dafawane balofede dunudafa!” Amalalu, hina bagade dunu udiana da Ilaisiama afia: i.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Ilaisia da Isala: ili hina bagadema amane sia: i, “Abuliba: le na da di fidima: bela: ? Di da asili, dia ada amola ame ilia balofede eno ilima adole ba: i. Ilima adole ba: la masa.” Youla: me da amane adole i, “Hame mabu! Hina Gode Hi fawane da nini hina bagade udiana amo Moua: be hina bagade nini hasalasimusa: asunasi.”
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Ilaisia da bu adole i, “Na da Hina Gode Esalebe Ea hawa: hamosa. Amo Ea Dioba: le, na da amane ilegele sia: sa. Na da dia fidisu dunu, Yuda hina bagade Yihosiafa: de, ema asigiba: le fawane, di fidimu.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Wali, sani baidama dusu dunu, nama oule misa!” Sani baidama dusu dunu da ea sani baidama dunanoba, Hina Gode da Ilaisiama Ea gasa i.
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 E amane sia: i, “Hina Gode da amane sia: sa, ‘Amo hano logo hafogai ganodini, hano ogai bagohame ogane gagama!
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Dilia da gibu amola fo afae hamedafa ba: mu. Be amo hafogai hano logo da hanoga nabai ba: mu. Amola di, amola dia ohe wa: i, amola liligi gaguli ahoasu ohe, ilia da hano manu gilisi ba: mu.”
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Ilaisia da eno amane sia: i, “Be amo hou hamomu da Hina Godema da asaboi gala. Amolawane, e da dilima Moua: bema hasalasisu hou imunu.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Dilia da ilia gagili sanawene moilai noga: idafa huluane amo hasalasilalu, samogene lamu. Dilia da ilia ifa dulu faili nasu huluane abusa: le salimu. Dilia da ilia hano nasu huluane lelesimu. Amola ilia nasegagi ha: i bugili nasu soge huluane gelega dedebole, gugunufinisimu.”
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Golale hahabe, hahabe gobele salalusu eso defele, hano da Idome sogeganini a: imisini, osobo dedeboi.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Moua: be dunu da hina bagade udiana ili doagala: musa: misi dagoi nababeba: le, ilia dunu huluane amo da gegesu liligi gaguli ahoasu dawa: , amo ilima misa: ne sia: nu, Isala: ili soge alalo amoga dadalema: ne sia: i.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Ilia da hahabe galu wa: legadole, eso da hano da: iya digagala: i amo da ma: ga: me agoai ba: i.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Moua: be dunu da amane sia: i, “Amo da maga: me! Ha lai wa: i udiana ilia da ili gobele gegeiba: le, huluane medole legei ba: sa. Ninia da ilia ha wa: i fisisuga liligi samogemusa: ahoa: di!”
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Be ilia da Isala: ili ha wa: i fisisua doaga: loba, Isala: ili dunu da ilima doagala: le, ili misibudili se bobogei. Ilia da ili se bobogele, Moua: be fi dunu medole lelegele,
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 amola ilia moilai gugunufinisi. Ilia da nasegagi sogebi amo baligilala, Isala: ili dunu huluane afae afae da amoga gelega gaga: lala, nasegagi ha: i manu bugili nasu soge huluane da gelega dedeboi ba: i. Amola ilia da hano bubuga: su huluane lelesisili amola ifa dulu faili nasu huluane abusa: le sali. Amalalu, fa: nodafa, Moua: be soge moilai bai bagade Ge Helese amo fawane dialebe ba: i. Isala: ili ga: muga: dadi gagui dunu da amo moilai sisiga: le, doagala: i.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Moua: be hina bagade da gegesu amoga e da hasalabe ba: beba: le, e da gegesu gobihei gagui dunu 7,000 agoane oule asili, ha wa: i dadalei amodili Silia hina bagade ema hobeale masusa: dawa: i. Be hamedei ba: i.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Amaiba: le, e da ea magobo mano lale (amo da e bagia hina bagade hamomu galu) amo medole legele, Moua: be ogogole ‘gode’ma, moilai gagoi da: iya gobele sali. Isala: ili dunu da amo ba: beba: le, bagade beda: igia: i. Amaiba: le, ilia da moilai fisili, ilia sogedafa buhagi.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Hina 3 >