< 1 Sa:miuele 11 >

1 Oubi afae baligili gomane, A:mone hina bagade Na: iha: sie da ea dadi gagui dunu bisili asili Gilia: de fi ganodini Ya: ibese moilai bai bagade fi ilima gegemusa: asi. Ya: ibese dunu da Na: iha: siema amane sia: i, “Dia ninima gousa: su hamoma. Amasea, dia da nini ouligima: mu.”
Nahash mutumin Ammon ya haura ya kewaye Yabesh Gileyad da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.”
2 Na: iha: sie da bu adole i, “Na da dilima gousa: su hamomu be hou afae fawane fa: no bobogemu. Na da dilia dunu huluane ilia lobodafadini si duga: le fasima: ne sia: sea fawane, na da dilima gousa: su hamomu. Amasea Isala: ili fi huluane da gogosiamu!”
Amma Nahash ya ce, “Zan ƙulla amana da ku kawai a kan sharaɗin cewa zan ƙwaƙulo idon dama na kowannenku, ta haka za a kunyata Isra’ila.”
3 Ya: ibese ouligisu hina ilia da amane sia: i, “Ninima eso fesuale ima! Amo esoga ninia da Isala: ili fi ganodini amo sia: sisa: i lamu. Amasea, ninia da fidisu dunu hame ba: sea, dima dia sia: i defele gousa: su hamomu.”
Dattawan Yabesh suka ce masa, “Ka ba mu kwana bakwai don mu aika manzanni a dukan ƙasar Isra’ila idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, za mu ba da kanmu gare ka.”
4 Amo sia: da Gibiaga Solo ea esaloba amoi doaga: i, amola amo sia: ilia sia: noba, dunu ilia da amo sia: nababeba: le hedolo dafawane heawini didigia: i.
Da manzannin suka zo Gibeya garin Shawulu, suka gaya wa mutane wannan sharaɗin, suka yi kuka mai zafi.
5 Amogalu, Solo hi bugi sogeanini ea bulamagau amola daeya hi diasu guda: mana didigia: be nababeba: le, e da adole ba: i, “Abuli hamoi? Abuliga dunu huluane da didigia: sala:” Ilia da sia: Ya: ibeseganini gaguli misi sia: amo adodole i.
A daidai wannan lokacin kuwa Shawulu yana dawowa daga gona tare da shanunsa na noma, sai ya ce, “Me ya faru, mutane suna kuka haka?” Sai suka faɗa masa abin da mutanen Yabesh suka faɗa musu.
6 Solo da amo sia: nababeba: le, Gode Ea A: silibu Hadigidafa da ema aligila sa: ili amola Solo da bagadewane ougi.
Da Shawulu ya ji, sa Ruhun Allah ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai.
7 E da bulamagau gawali aduna fane, fofonobone dadamui. Amalu bulamagau dadamui amo huluane sia: adola ahoasu dunu ilima i. Solo da sia: adodola ahoasu dunu ilima, amo bulamagau dadamui agoane Isala: ili fi soge huluanema olelela lama: ne iasi. Amoga ilia da dawa: digima: ne, e da amo sisasu sia: si, “Nowa dunu da Solo amola Sa: miuele elea gegena ahoabe amoga hame madelasea, ilia ohe fofoi amoga da agoane hamomu.” Sia: adola ahoasu dunu ilia da agoane sisia: Isala: ili soge ganodini lai. Isala: ili dunu ilia da Hina Gode Ea ilima adi hamoma: bela: le beda: i, amola ilia huluanedafa Soloma gilisili mafia: i.
Ya ɗauki shanu biyu, ya yayyanka su gunduwa-gunduwa, ya aika da su ko’ina a ƙasar Isra’ila ta wurin manzanni cewa, “Duk wanda bai fita ya bi Shawulu da Sama’ila ba, haka za a yi da shanunsa.” Mutanen suka ji tsoron Ubangiji suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda.
8 Solo da dunu huluane Bisege moilaiga gegedolesi, dunu da ba: loba 300,000 agoane da Isala: ili dunu amola 30,000 agoane da Yuda dunu agoane ba: i.
Mutanen Isra’ila sun kai dubu ɗari uku. Mutanen Yahuda kuma dubu talatin, sa’ad da Shawulu ya tara su a Bezek.
9 Ilia da Ya: ibese dunu sia: adola misi ilima amane sia: i, “Dia dunuma sia: ma. Aya eso dagobe galu ili da gaga: i ba: mu.” Ya: ibese dunu ilia da amo sia: nababeba: le, ilia da baligili bagade nodoi.
Suka ce wa’yan aikan da suka zo, “Ku faɗa wa mutanen Yabesh Gileyad, ‘Gobe, kafin rana tă yi zafi, za ku sami ceto.’” Sa’ad da’yan aikan suka tafi, suka ba da saƙon nan ga mutanen Yabesh, sai suka farin ciki.
10 Amalu ilia da Na: iha: siema amane sia: i, “Aya da dia nini lama: mu, amalu di adi hanai ninima hamomusa: dawa: sea, hamoma: mu.”
Suka ce wa Ammonawa, “Gobe za mu miƙa wuya gare ku, ku kuma yi duk abin da kuka ga dama.”
11 Amo gasia, Solo da ea dadi gagui dunu udiana mogi. Golale, hahabedafa, ilia da ha lai diasua hehenaia gugudili sa: ili, A:mone dunu huluane doagala: le, eso dogoa, A:mone dunu huluane da medole legei dagoi ba: i. Dunu hame bogogia: i esafulu, ilia da afagogole, dunu hisu hobeale afia: i.
Gari yana wayewa, sai Shawulu ya raba mutane kashi uku, a sa’a ta ƙarshe na daren sai suka fāɗa wa sansanin Ammonawa, suka kuma karkashe su har lokacin da rana ta yi zafi. Waɗanda suka kuɓuce kuwa suka warwatsu, har babu biyunsu da aka bari tare.
12 Isala: ili dunu ilia da Sa: miuelema amane sia: i, “Dunu amo da Solo ea hina hamoma: ne hame dawa: i amo da habila: ? Amo dunu ninia fanelegemusa: , ninima oule misa!”
Sai mutane suka ce wa Sama’ila, “Su wa suka ce, ‘Shawulu zai yi mulkinmu?’ A kawo mana su mu kashe.”
13 Be Solo da amane sia: i, “Ninia da dunu afae da wali hamedafa fane legemu. Bai wali eso, Hina Gode da Isala: ili dunu gaga: i dagoi.”
Shawulu ya ce, “Ba wanda zai mutu yau, gama Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana.”
14 Amalu, Sa: miuele da ilima amane sia: i, “Ninia da bu Giliga: lega gilisili, bu Solo da ninia hina bagade asulimu.”
Sai Sama’ila ya ce wa mutane, “Ku zo mu tafi Gilgal, a can za a yi wankan sarauta.”
15 Amaiba: le, ilia da huluane Giliga: le moilaiga asili, hadigi sogea amoi Solo da ilia hina bagade asuli. Ilia da Hahawane Gilisili Olofole Iasu gobele salasu hamonanu, Solo amola Isala: ili dunu huluane ilia da hahawane gilisisu hamoi.
Don haka dukan mutane suka tafi Gilgal, suka tabbatar da Shawulu sarki a gaban Ubangiji. A can suka miƙa hadaya ta salama a gaban Ubangiji, Shawulu kuwa da dukan Isra’ila suka yi babban liyafa.

< 1 Sa:miuele 11 >