< المَزامِير 116 >
إِنِّي أُحِبُّ الرَّبَّ لأَنَّهُ يَسْمَعُ ابْتِهَالِي وَيَسْتَجِيبُ إِلَى تَضَرُّعَاتِي. | ١ 1 |
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
أَمَالَ أُذُنَهُ إِلَيَّ لِذَلِكَ أَدْعُوهُ مَادُمْتُ حَيًّا. | ٢ 2 |
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
طَوَّقَتْنِي حِبَالُ الْمَوْتِ. أَطْبَقَ عَلَيَّ رُعْبُ الْهَاوِيَةِ. قَاسَيْتُ ضِيقاً وَحُزْناً. (Sheol ) | ٣ 3 |
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
فَدَعَوْتُ الرَّبَّ: آهِ يَا رَبُّ نَجِّ نَفْسِي! | ٤ 4 |
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
الرَّبُّ حَنُونٌ وَبَارٌّ. إِلَهُنَا رَحِيمٌ. | ٥ 5 |
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
الرَّبُّ حَافِظُ الْبُسَطَاءِ. تَذَلَّلْتُ فَخَلَّصَنِي. | ٦ 6 |
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
عُودِي يَا نَفْسِي إِلَى طُمَأْنِينَتِكِ، لأَنَّ الرَّبَّ قَدْ أَحْسَنَ إِلَيْكِ. | ٧ 7 |
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
لأَنَّكَ يَا رَبُّ أَنْقَذْتَ نَفْسِي مِنَ الْمَوْتِ، وَعَيْنِي مِنَ الدَّمْعِ، وَقَدَمَيَّ مِنَ التَّعَثُّرِ، | ٨ 8 |
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
لِذَلِكَ أَسْلُكُ بِطَاعَةٍ أَمَامَ الرَّبِّ فِي دِيَارِ الأَحْيَاءِ. | ٩ 9 |
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
آمَنْتُ لِذَلِكَ تَكَلَّمْتُ. أَنَا عَانَيْتُ كَثِيراً. | ١٠ 10 |
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
وَقُلْتُ فِي حَيْرَتِي: «جَمِيعُ الْبَشَرِ كَاذِبُونَ». | ١١ 11 |
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
مَاذَا أَرُدُّ لِلرَّبِّ مُقَابِلَ كُلِّ مَا أَبْدَاهُ نَحْوي مِنْ حُسْنِ الصَّنِيعِ؟ | ١٢ 12 |
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
سَأَتَنَاوَلُ كَأْسَ الْخَلاصِ، وَأَدْعُو بِاسْمِ الرَّبِّ. | ١٣ 13 |
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
أُوْفِي نُذُورِي لِلرَّبِّ أَمَامَ كُلِّ شَعْبِهِ. | ١٤ 14 |
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
عَزِيزٌ فِي عَيْنَي الرَّبِّ مَوْتُ قِدِّيسِيهِ. | ١٥ 15 |
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
آهِ يَا رَبُّ أَنَا عَبْدُكَ. أَنَا عَبْدُكَ وَابْنُ أَمَتِكَ. أَنْتَ حَلَلْتَ قُيُودِي. | ١٦ 16 |
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
لَكَ أُقَدِّمُ ذَبَائِحَ الشُّكْرِ، وَأَدْعُو بِاسْمِكَ. | ١٧ 17 |
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
أُوْفِي نُذُورِي لِلرَّبِّ أَمَامَ كُلِّ شَعْبِهِ. | ١٨ 18 |
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
فِي دِيَارِ بَيْتِ الرَّبِّ، فِي وَسَطِكِ يَا أُورُشَلِيمُ. هَلِّلُويَا. | ١٩ 19 |
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.