< المَزامِير 113 >

هَلِّلُويَا. سَبِّحُوا يَا عَبِيدَ الرَّبِّ، سَبِّحَوا اسْمَ الرَّبِّ. ١ 1
Yabi Ubangiji. Ku yabe shi, ya ku bayin Ubangiji, ku yabi sunan Ubangiji.
لِيَكُنِ اسْمُ الرَّبِّ مُبَارَكاً مِنَ الآنَ وَإِلَى الأَبَدِ. ٢ 2
Bari a yabi sunan Ubangiji, yanzu da har abada kuma.
لِيُسَبَّحْ بِاسْمِ الرَّبِّ مِنْ مَشْرِقِ الشَّمْسِ إِلَى مَغْرِبِهَا. ٣ 3
Daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa, a yabi sunan Ubangiji.
الرَّبُّ مُتَسَامٍ عَلَى جَمِيعِ الأُمَمِ، وَمَجْدُهُ فَوْقَ السَّمَاوَاتِ. ٤ 4
Ana ɗaukaka Ubangiji a bisa dukan al’ummai, ɗaukakarsa a bisa sammai
مَنْ هُوَ نَظِيرُ الرَّبِّ إِلَهِنَا السَّاكِنِ فِي الأَعَالِي؟ ٥ 5
Wane ne yake kamar Ubangiji Allahnmu, Wannan mai zama a kursiyi can bisa,
الْمُطِلِّ مِنْ عَلْيَائِهِ إِلَى أَسْفَلَ لِيَرَى السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضَ. ٦ 6
wanda yake sunkuya yă dubi sammai da duniya?
يُنْهِضُ الْمِسْكِينَ مِنَ التُّرَابِ، وَيَرْفَعُ الْبَائِسَ مِنْ الْمَزْبَلَةِ، ٧ 7
Yakan tā da matalauta daga ƙura yakan ɗaga mabukata daga tarin toka;
لِيُجْلِسَهُ مَعَ أَشْرَافِ شَعْبِهِ. ٨ 8
ya zaunar da su tare da sarakuna, tare da sarakunan mutanensu.
يَرْزُقُ العَاقِرَ أَوْلاداً. يَجْعَلُهَا أُمّاً سَعِيدَةً. هَلِّلُويَا. ٩ 9
Yakan zaunar da matar da ba haihuwa a gidanta ta zama kamar mahaifiyar’ya’ya mai farin ciki. Yabi Ubangiji.

< المَزامِير 113 >