< Luka 16 >

1 Yesu kuru a woro nono katwa me, “Umong unan nikurfung wadi nin nang tamani me, ida belinghe unang yeujun ntamanie din nanzu unis.
Yesu ya kuma ce wa almajiransa, “Akwai wani mai arziki da yake da wakili, sai aka yi karan sa da cewa wannan wakili yana fallasar masa da dukiya.
2 Unan nikurfughe yicila ghe aworoghe, 'I yanghari ndin lanze litife? Daa uda nyii kibatiza nimon ile na nwa nili uyenje bana na fe unit ucineari ba.'
Sai mai arziki ya kira shi ya ce masa, 'Labarin me nake ji game da kai? Kawo lissafin wakilcin ka, don ba za ka sake zama wakili na ba.'
3 Unan yenjughe ntamane woro letime, 'I yanghari mbati nin litining, I yanghari mba ti, bara na cikilari nighe ma kalu katwa kane nacara nighe? Na indi nin likava mawuzu wuzu ba, tutung indi lanzu incin kufili.
Sai wakilin ya ce a ransa, 'Kaka zan yi, da yake maigida na zai karbe wakilci daga hannuna? Gashi, ba ni da karfin noma ina kuwa jin kunya in yi roko.
4 In yiru imon ile na mba ti, bara na lwa kala katwa kane nacara nighe, anit ma sesui ngamine.'
Na san abin da zan yi domin idan an fitar da ni daga wakilcin, mutane su karbe ni a gidajensu.
5 Unan yeujun ntamane yicila vat nale na cikilare din durtu nami tire, anin tirino unan burne, 'Imashinari cikilare din durtu fi?'
Sai wakilin ya kira kowanne daya da maigidansa ke bi bashi, yace wa na farkon, 'Nawa maigida na yake bin ka?'
6 A woro, 'A mudu akut likure nnuf kuca.' Anin waroghe 'Soo mas, kibatiza fe kaa, u nyertin akut ataun.'
Ya ce, 'Garwan mai dari.' Sai ya ce masa, 'Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubuta hamsin.'
7 Unang yeuju ntamane woro mmong, 'I mashinari idin durtufi?' A woro, 'A mudu akut likure nialkama.' A woroghe 'Kibatiza fe kanga yertina akut likure sa aba.'
Ya kuma ce wa wani, 'Nawa ake binka?' Ya ce, 'Buhu dari na alkama.' Ya ce masa, 'Ga tarkardarka, ka rubuta tamanin.'
8 Unan nikurfughe taghe njah bara na awa su katwa me caut ba, bara na nono nyii ulele di nin nibinai nsu nimon icine bara anit mime ba na nafo nonon nkananghe di. (aiōn g165)
Sai maigida ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama 'ya'yan zamanin nan a ma'ammalar su da mutanen zamaninsu sun fi 'ya'yan haske wayo. (aiōn g165)
9 In belin fi, pizira adondong bara litife nin nimon nyii, bara I wa nyaa ima pirizin fi nanya nilari mi ne. (aiōnios g166)
Ina gaya maku ku yi abuta ta dukiya ta rashin gaskiya, saboda idan ya kare, su karbe ku a gidaje masu dauwama. (aiōnios g166)
10 Ule na adi nin yinnu-sa-uyenu nanya nimon baat ade nin yinnu-sa-uyenu nanya ni dya, ule na adi nin salin yinnu-sa-uyenu nanya ni baat na ama yitu nin yinnu-sa-uyenu nanya nimon idya ba.
Wanda yake da aminci a karamin abu, mai aminci ne a babban abu, wanda yake marar gaskiya a karamin abu, marar gaskiya ne a babban abu.
11 Bara nani, andi na udi nin yinna-sa-uyenu nimoon inyii ba, ghari ba yinnu ninfi nin nimoon kidegene?
Idan fa ba ku yi aminci da dukiya mara adalci ba, wa zai amince maku da dukiya ta gaskiya?
12 Nanere, andi na udi nin yinnu-sa-uyenu kitene kuturan mong ba, ghari ma nifi ile na idi infe?
Idan kuma ba ku yi aminci da kudin wani ba, wa zai ba ku kudin da ke naku?
13 Na kucin wasaa amyino an cin nilara naba kubi kurume ba, sa a ma nari umong ati usun mmong, sa a su umong katwa amari usun mmong, na u wasa usu Kutelle licin nin tamani kubi kurume ba.”
Ba bawan da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya ko kuwa ya amince wa dayan, ya raina dayan. Ba za ku iya bauta wa Allah ku kuma bauta wa dukiya ba.”
14 Afarsayawe na i wadi anam su nikurfunghari, I lanza ule ulire vat, itunna nsisu ghe.
Da Farisawa da ke da kaunar kudi suka ji dukan wadannan abubuwa, suka yi masa ba'a.
15 A woro nani, “Idin suzu kidegen mine niyizi nanitari, bara nani Kutelle yiru nibinai mine. Ileli imon na idin ruu ining idi zemzem nizi Kutelle.
Sai ya ce masu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abin da mutane suke girmamawa kwarai abin kyama ne a gun Allah.
16 Uduka nin nanan liru nin nuu Kutelle wa di, Yohana nin daa. Unuzun koni kubi udu sa ligang, uliru Kutelle idim belun nin, vat nanit din shoo ati nanya ti bau ti bau.
Attaura da litattafan annabawa suna nan har zuwan Yahaya. Tun daga lokacin nan ake yin bisharar mulkin Allah, kowa kuma yana kokarin kutsawa zuwa cikinta.
17 Bara nani ukatin nin sauki nworu kitene kani nin kadas kata nin waru fiyert firum nanyan nliru me ikala sa uti kinuu.
Duk da haka, zai fi sauki sama da kasa su shude, da ko digo daya na attaura ya shude.
18 Vatin nlenge na akoo uwani me ayira umong adin nozu nin na wani ahem, nanere uwani ule na akoo ules me aminin di yira umong adin nozu nin les uhem.
Duk wanda ya saki matansa ya auri wata ya aikata zina, kuma wanda ma ya auri sakakkiya ya aikata zina.
19 Umong unan nikurfung wa duku na iwa shonghe imoon icine anin din lanzun mmang vat liri nanya ntamani udya.
Akwai wani mai arziki, mai sa tufafi na alfarma masu tsada yana shagalin sa kowace rana.
20 Umong unan kufilli nunnu kibulung me nin nanut kidowo me.
Aka ajiye wani gajiyayye a kofarsa, mai suna liazaru wanda duk jikinsa miki ne,
21 A wadin su a li mbubun nimon li na idin disu kuteen, banin nani, ninau nin din lelu anut kidowo me.
Shi kuwa yana marmarin ya koshi da barbashin da ke fadowa daga teburin mai arzikin nan har ma karnuka sukan zo suna lasar mikinsa.
22 Usuo inlong liyiri unam kufille kuu anan kadura Kutelle da yiraghe udu abunu Ibrahim. Unam nikurfughe wang kuu ikasaghe.
Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, malaiku kuma suka dauke shi suka kai shi wurin Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi,
23 Nanyan nla, adin niu, a fiya iyisi me ayene Ibrahim ku piit nin Liazaru figiri me. (Hadēs g86)
yana cikin hades yana shan azaba, sai ya daga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a kirjinsa. (Hadēs g86)
24 A fiya liwai me aworo, 'Ibrahim ucif lanza nkune-kune ning utuu Liazaru ku, a diti liyicin me nanyan myen adak ada tii limila cancam, indin niu namyan nla ulele.'
Sai ya yi kira ya ce, 'Baba Ibrahim, ka ji tausayi na, ka aiko Li'azaru ya tsoma dan yatsansa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.'
25 Bara nani Ibrahim woro, 'Gono kubin laife uwa seru imon icine nlaife, Liazaru sere imon inanzang. Bara nani itaghe insheu kibinai kikane, fe tutung uniu.
Amma Ibrahim ya ce, 'Yaro, ka tuna fa a zamanka na duniya ka sha duniyarka, ka kuma karba abubuwa masu kyau, amma Li'azaru kuma sai wahala. Amma yanzu dadi ake bashi a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 Banin nani kuwu kudya nkese nari bara na alenge na ima kafinu udu kiti fe na iwasa i kafina ba, a na umong wasa a kafina udak kiti bite ba.
Banda haka ma, akwai rami mai zurfi, domin wadanda suke son ketarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ketaro zuwa wurinmu daga can.'
27 Unan nikurfughe woro, 'Ndin foo fi nacara, Ibrahim ucif. U tuughe udun ngan cif nighe.
Sai mai arziki ya ce, 'To ina rokonka, Baba Ibrahim, ka aike shi zuwa gidan mahaifina -
28 Bara na idi nin nwana inung nataun bara anan wunno nani atuf, bara iwa dak imus kitin niu kaane tutung.'
domin ina da 'yan'uwa maza biyar, ya je ya yi masu gargadi kada su ma su zo wurin azaban nan.'
29 Bara nani Ibrahim woro, 'Idi nin Musa nan nanan liru nin nuu Kutelle; na ilanza nani.'
Amma Ibrahim ya ce, 'Suna da Musa da annabawa; bari su saurare su.'
30 Unan nikurfunghe kpana aworo, 'na nanere ba, Ibrahim ucif, bara nani iwase umong ulenge na aba du kitimene nanya nabi, I ma kpiliu nibinai mine.'
Sai mai arziki ya amsa, 'A'a, Baba Ibrahim, idan wani daga cikin matattu ya je wurinsu, zasu tuba.'
31 Bara nani Ibrahim woroghe, 'Andi na ima lanzu Musa ku nan nanan liru nin nuu Kutelle ba, na ima lanzu umong tutung ba sa afita nanya nani.'”
Amma Ibrahim ya ce masa, 'In dai har basu saurari Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su rinjayu ba.'”

< Luka 16 >