< Ts'etta ıxhaynbı 50 >
1 Yusuf dekkılqa k'yorzul geşşe-geşşe mang'us ubbabı ha'a.
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 Mang'vee cune g'ulluxçiy-doxturaaşilqa dekkın mayit mumyelamişe'ecenva əmr haa'a. Doxturaaşed İzrailin mayit mumyelamişa'an.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 Mana iş doxturaaşe yoq'ts'al yiğna haa'a. Mumyelamişa'as manimena vaxtniyxhe vukkiykanna. Yights'al yiğna misirğançenbı mang'uqa gyaaşe.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 Ak'ın yiğbı ç'əveetxhamee, Yusufee fironne insanaaşik'le eyhen: – Zı vuşde ulen aqqıxheene fironuk'le eyhe,
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 dekke zasqa k'ın g'assaras alikkı uvhuynniy: «Zı qik'asda xhinne vor. Kana'anne ölkee zı zasda mağaree nyaq'v hav'u. Zı maa k'eyxhe». Həşde fironee zı hasrecen, dek k'eyxhı yı'q'əlqa sak'alas.
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 Fironee eyhen: – Dekke nəxdiy vasqa k'ın g'assaras alikkı, həməxürur mana k'eyxhe.
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 Məxür Yusuf ayk'anna dek k'eyxhas. Yusufuka sacigee fironun delesın insanar, Misirın ağsaqqalar,
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 Yusufneyiy dekkıne xaabın gırgınbı, çocar, havayk'an. Manbışe saccu çavra-vəq'əyiy uşaxar Goşen g'alyaa'a.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 Manbışika sacigee balkanaaşil alepxıynbı, dəv'əys hı'iyne daşk'abışe gyuv'uruynbı yəqqı'lqa qığeebaç'e. Maa qəpqəs-ələpqəs devxhesınmeen insanar vooxhe.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 Manbı İordan damayne şene sural, Atad eyhene cigeene atteeqa (suk mettaa'an ciga) hipxhıring'a, axtıne nıq'ıka gyaaşe giviyğal. Ma'ab Yusufee dekkıs yighılle yiğna ak' hoole.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 Mane ölkayne insanaaşik'le Kana'anğançenbışik'le, Atadee hoolena ak' g'avcumee, uvhuyn: «Misirbışiqa xədın geşşuyud». İordan damayne k'anene cigays çil-alla Avel-Mitsrayim (misirbışin geşşuy) do giyxhe.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 Yaaq'ubne dixbışe gırgın dekke uvhuyn xhinne ha'a.
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 Mana manbışe Kana'anee ölkeeqa qarı, Mamreys k'anene Maxpela eyhene çoleene mağaree'ar nyuq'neeqa giyxhe. Mana mağara İbrahimee çoluka sa cigee cus nyaq'v haa'asın ciga ixhecenva Q'etbışda eyxhene Efronukeniy alivşu.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 Dek k'eyxhıyle qiyğa, Yusuf cune çocaaşika, dekkıne ak'ıs abıyne gırgınbışika sacigee Misirqa siyk'al.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 Dek qik'uyle qiyğa, Yusufne çocaaşe sana-sang'uk'le eyhen: – Yusufee şi hı'iynçina qəl yik'el avqu vuxhee, mana qəl şake qığaahas vukkiykıne, şi hucoone ha'as?
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 Mançil-allab manbışe Yusufus xabar g'axuvu: – Dekkee qik'asse şak'le uvhuynniy:
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 «Yusufuk'le inəxüd eyhe: „Hucoone ixhes, çocaaşe vas hav'una pisvalla, yik'el hivxhanee'e“». Həşded şi vake heqqa, hucoone ixhes, yiğne dekkee ı'bəədat ha'ane Allahee g'ulaaşin bınahbı yik'elixan he'ecen. Man eyhenbı Yusufuk'le g'ayxhımee, geşşe giyğal.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 Qiyğa çocar mang'usqa abı çiyelqamee k'yobzur, «Şi həşdiyle yuğun g'ular vobva» eyhe.
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 Yusufee manbışik'le eyhen: – Zı nya'a Allahne vor, şu zale qəvəəq'ənas?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 İlyaake, şos zas pisvalla haa'as vukkiykın, Allaheeyib mana yugvalis qav'u. G'iyna şok'le g'ecenbıyiy xəppanane insanaaşina ı'mı'r g'attivxhan he'ecenva Allahee məxüd hı'ı.
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 Mançil-alla qıməəq'ən zı şoqar vuşde uşaxaaşiqar ilyakkasda. Yusuf manbışiqa g'üvənara yuşanı'ı manbışis yik'bı hele.
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 Yusuf cuneyiy dekkıne xizanıka Misir axva. Yusufee vəşşe yits'ılle sen ha'a.
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 Mang'uk'le Efrayimın uşaxarıb nevabıb g'oocenbı. Menaşşeyne duxayne Maxiriyne uşaxaaşisıb mang'vee dekvalla haa'a.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 Sabara gah ılğevç'uyle qiyğa Yusufee çocaaşik'le eyhen: – Yizda qik'asda gah k'ane quvxheeyib, Allahee şu yik'el hivxanaa'as deş. Allahee şu ine ölkeençe qığaa'asınbı. Mang'vee k'ın g'assır İbrahimıs, I'saq'ıs, Yaaq'ubus hevlesva uvhiyne cigeeqa şu quvkees.
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 Qiyğa Yusufee İzrailybışisqa k'ınbı g'assaras alikkı eyhen: – Allahee şos huvuyn cuvab mısacad yik'el hixan ha'as deş. Şunad əlyhəəng'ə, yizın bark'vbı inyaa g'ılyma'a, şoka qıkkee.
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 Yusuf vəşşe yits'ılle sen hı'ı qek'a. Mana Misiree mumyelamiş hı'ı tabuteeqa giyxhe.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.