< Nehemia 1 >

1 Maneno ya Nehemia mwana wa Hakalia Ikawa, katika mwezi wa Kisleu, katika mwaka wa ishirini, nilikuwa katika mji mkuu wa Sushani,
Kalmomin Nehemiya ɗan Hakaliya. A cikin watan Kisleb a shekara ta ashirin, yayinda nake a fadar Shusha.
2 mmoja wa ndugu zangu, Hanani, alikuja pamoja na watu wengine kutoka Yuda, nami nikawauliza kuhusu Wayahudi waliopona, Wayahudi waliosalia waliokuwa huko, na kuhusu Yerusalemu.
Hanani, ɗaya daga cikin’yan’uwana, ya zo daga Yahuda tare da waɗansu mutane. Na kuwa tambaye shi game da raguwar Yahudawan da suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta, da kuma game da Urushalima.
3 Wakaniambia, “Wale waliokuwa katika mkoa ule waliookoka katika kifungo wapo katika shida kubwa na aibu kwa sababu ukuta wa Yerusalemu umebomolewa na milango yake imeteketezwa kwa moto.”
Suka ce mini, “Waɗanda suka tsira daga kwasan zuwa zaman bauta da kuma suka komo cikin yankin suna cikin babban damuwa da wulaƙanci. An rushe katangar Urushalima aka kuma ƙone ƙofofin da wuta.”
4 Na mara tu niliposikia maneno haya, nikakaa na kulia, na kwa siku niliendelea kuomboleza na kufunga na kuomba mbele ya Mungu wa mbinguni.
Da na ji waɗannan abubuwa, sai na zauna na yi kuka. Na yi kwanaki ina makoki da azumi, na kuma yi addu’a a gaban Allah na sama.
5 Ndipo nikasema, “Wewe ndiwe Bwana, Mungu wa mbinguni, Mungu uliye mkuu na kushangaza, unayetimiza agano na upendo wa kudumu pamoja na wale wanaokupenda na kushika amri zake.
Na ce, “Ya Ubangiji Allah na sama, Allah mai girma da mai banrazana, wanda yake kiyaye alkawarinsa na ƙauna da waɗanda suke ƙaunarsa, suke kuma yin biyayya da umarnansa,
6 Sikiliza maombi yangu na fungua macho yako, ili uisikie sala ya mtumishi wako kwamba sasa nasali mbele yako mchana na usiku kwa ajili ya watu wa Israeli watumishi wako. Mimi ninakiri dhambi za watu wa Israeli, ambazo tumefanya dhidi yako. Wote mimi na nyumba ya baba yangu tumefanya dhambi.
ka sa kunne ka kuma buɗe idanunka ka ji addu’ar da bawanka yake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra’ila. Na furta zunuban da mu Isra’ilawa, har da ni da kuma gidan mahaifina muka yi maka.
7 Tumefanya uovu sana juu yako, na hatukuzingatia amri, sheria, na hukumu ambazo ulimwamuru mtumishi wako Musa.
Mun yi mugunta gare ka. Ba mu yi biyayya da umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da ka ba wa bawanka Musa ba.
8 Tafadhali kumbuka neno ulilomuamuru mtumishi wako Musa, 'mkitenda pasipo uaminifu, nitawatawanya kati ya mataifa,
“Ka tuna da umarnan da ka ba wa bawanka Musa, kana cewa, ‘In kun yi rashin aminci, zan warwatsar da ku a cikin al’ummai,
9 lakini mkirudi kwangu na kufuata amri zangu na kuzifanya, ingawa watu wako walienea chini ya mbingu za mbali, Nami nitawakusanya kutoka huko na kuwaleta mahali pale nilipopachagua ili kulifanya jina langu.'
amma in kuka dawo gare ni kuka kuma yi biyayya da umarnaina, to, ko mutanenku da aka kwasa zuwa zaman bauta suna can wuri mafi nisa, zan tattara su daga can in kawo su wurin da na zaɓa yă zama wurin zama don Sunana.’
10 Sasa wao ni watumishi wako na watu wako, ambao uliwaokoa kwa nguvu yako kubwa na kwa mkono wako wenye nguvu.
“Su bayinka ne da kuma mutanenka da ka fansa ta wurin ƙarfinka mai girma da kuma hannunka mai iko.
11 Bwana, naomba, sikiliza sasa maombi ya watumishi wako na sala ya watumishi wako ambao hufurahia kuheshimu jina lako. Sasa unifanikishe mimi mtumishi wako leo, na unijalie rehema mbele ya mtu huyu.” Nilikuwa mnyweshaji wa mfalme.
Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu’ar wannan bawanka da kuma ga addu’ar bayinka waɗanda suke farin cikin girmama sunanka. Ka ba wa bawanka nasara a yau ta wurinsa yă sami tagomashi a gaban wannan mutum.” Ni ne mai riƙon kwaf sarki.

< Nehemia 1 >