< Salmos 15 >
1 Señor, ¿quién puede habitar en tu templo, quién puede residir en tu santo monte?
Zabura ta Dawuda. Ubangiji, wa zai zauna cikin wuri mai tsarkinka? Wa zai zauna a kan tudunka mai tsarki?
2 El que sigue su camino con integridad, haciendo justicia, y diciendo lo que es verdad en su corazón;
Sai wanda ba shi da laifi kuma yana yin abin da yake daidai, wanda yake faɗin gaskiya daga zuciyarsa
3 Él que no dice mentira. él que no hace mal a su amigo, ni ofende a su prójimo.
ba ya kuwa ɓata sunan wani da harshensa, wanda ba ya yi wa maƙwabcinsa mugunta ba ya kuwa baza jita-jita a kan ɗan’uwansa,
4 Él que honra a los que temen al Señor, él que se aparta de aquel que no tiene la aprobación del Señor, él que hace un juramento contra sí mismo, y no por eso cambia.
wanda yake ƙin mugun mutum amma yakan girmama masu tsoron Ubangiji, yakan cika alkawarinsa ko da ma ya zafe shi,
5 El que no presta su dinero por intereses, Ni acepta soborno en contra del inocente. El que hace estas cosas nunca será movido.
wanda yake ba da rance ba tare da ruwa ba kuma ba ya karɓan cin hanci don yă kā da marar laifi. Shi wanda yake yin waɗannan abubuwa ba zai taɓa jijjiguwa ba.