< Isaías 59 >

1 En verdad, la mano del Señor no se ha acortado, por lo que no puede dar la salvación; y su oído no está cerrado para oír:
Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
2 Pero tus pecados se han interpuesto entre ti y tu Dios, y por tus malas acciones su rostro ha sido ocultado, de modo que no te dará respuesta.
Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
3 Porque tus manos están inmundas de sangre, y tus dedos de pecado; tus labios han dicho cosas falsas, y tu lengua engaña.
Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
4 Nadie presenta una causa recta, ni da una decisión verdadera; su esperanza es engañosa y sus palabras son falsas; Están engendrados con el pecado, y dan a luz al mal.
Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
5 Dan a luz huevos de serpiente, y hacen hilos de araña; el que toma sus huevos para comer, muere, y el huevo triturado se convierte en una serpiente venenosa.
Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
6 Sus hilos retorcidos no harán ropa, y sus obras no les darán nada para cubrirse a sí mismos; sus obras son obras de pecado, y los actos violentos están en sus manos.
Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
7 Sus pies van rápidamente al mal, y se deleitan en la muerte de los rectos; sus pensamientos son pensamientos de pecado; El derroche y la destrucción están en sus caminos.
Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
8 No tienen conocimiento del camino de la paz, y no tienen sentido de lo que es correcto en su comportamiento; se han forjado caminos que no son rectos; el que entra en ellos no tiene conocimiento de la paz.
Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
9 Por esta causa nuestro derecho está lejos de nosotros, y la justicia no nos alcanza; estamos buscando la luz, pero solo existe la oscuridad; resplandor, pero andamos en la oscuridad.
Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
10 Seguimos nuestro camino, como hombres ciegos que buscan la pared, como aquellos que no tienen ojos; corremos contra las cosas a la luz del día como si fuera de noche; Nuestro lugar está en la oscuridad como hombres muertos.
Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
11 Hacemos ruidos de dolor, como osos, y sonidos tristes como palomas: estamos buscando nuestra justicia, pero no está allí; por la salvación, pero está lejos de nosotros.
Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
12 Porque nuestras malas acciones aumentan delante de ti, y nuestros pecados dan testimonio contra nosotros; porque nuestras malas acciones están con nosotros, y tenemos conocimiento de nuestros pecados.
Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
13 Hemos ido en contra del Señor y hemos sido falsos con él, apartándonos de nuestro Dios, nuestras palabras han sido descontroladas y en nuestros corazones hay pensamientos de engaño.
tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
14 Y el derecho se ha vuelto atrás, y la justicia está muy lejos; porque la buena fe no se ve en los lugares públicos, y la verdad tropezó en la plaza. El comportamiento recto no puede entrar.
Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
15 Sí, la fe se ha ido; y aquel cuyo corazón se ha vuelto del mal, llega al poder de los crueles; y el Señor lo vio, y se enojó de que no había nadie para defender su causa.
Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
16 Y vio que no había hombre, y se sorprendió de que no hubiera nadie que les ayudara; así que su brazo dio la salvación, e hizo justicia con su apoyo.
Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
17 Sí, se puso la justicia como una coraza, y la salvación como un casco; y se puso el castigo como vestimenta, y la ira como un manto.
Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
18 Él les dará la recompensa correcta de sus actos, la ira a sus atacantes, el castigo a sus enemigos, e incluso en las islas enviará el castigo.
Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
19 Entonces verán el nombre del Señor desde el oeste, y su gloria desde el este, porque vendrá como una corriente apresurada, forzada por un viento del Señor.
Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
20 Y como salvador vendrá a Sión, y de todos los descendientes de Jacob que se arrepientan de sus culpas, dice el Señor.
“Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
21 Y en cuanto a mí, este es mi acuerdo con ellos, dice el Señor: mi espíritu que está sobre ti, y mis palabras que he puesto en tu boca, no se irán de tu boca ni de tu simiente, o de la boca de tu simiente, dice el Señor, desde ahora y por siempre.
“Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.

< Isaías 59 >