< Salmos 105 >

1 Louvai ao Senhor, e invocai o seu nome; fazei conhecidas as suas obras entre os povos.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Cantai-lhe, cantai-lhe salmos: falai de todas as suas maravilhas.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glóriai-vos no seu santo nome: alegre-se o coração daqueles que buscam ao Senhor.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Buscai ao Senhor e a sua força: buscai a sua face continuamente.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Lembrai-vos das maravilhas que fez, dos seus prodígios e dos juízos da sua boca;
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 Vós, semente de Abraão, seu servo, vós, filhos de Jacob, seus escolhidos.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Ele é o Senhor, nosso Deus; os seus juízos estão em toda a terra.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Lembrou-se do seu concerto para sempre, da palavra que mandou a milhares de gerações.
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 O qual concerto fez com Abraão, e o seu juramento a Isaac.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 E confirmou o mesmo a Jacob por estatuto, e a Israel por concerto eterno,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 Dizendo: A ti darei a terra de Canaan, a sorte da vossa herança.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Quando eram poucos homens em número, sim, mui poucos e estrangeiros nela.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Quando andavam de nação em nação e dum reino para outro povo.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Não permitiu a ninguém que os oprimisse, e por amor deles repreendeu a reis, dizendo:
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Não toqueis os meus ungidos, e não maltrateis os meus profetas.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Chamou a fome sobre a terra, quebrantou todo o sustento do pão.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Mandou perante eles um varão, José, que foi vendido por escravo:
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Cujos pés apertaram com grilhões: foi metido em ferros:
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Até ao tempo em que chegou a sua palavra; a palavra do Senhor o provou.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Mandou o rei, e o fez soltar; o governador dos povos, e o soltou.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Fê-lo senhor da sua casa, e governador de toda a sua fazenda;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Para sujeitar os seus príncipes a seu gosto, e instruir os seus anciãos.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Então Israel entrou no Egito, e Jacob peregrinou na terra de Cão.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 E aumentou o seu povo em grande maneira, e o fez mais poderoso do que os seus inimigos.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Virou o coração deles para que aborrecessem o seu povo, para que tratassem astutamente aos seus servos.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Enviou Moisés, seu servo, e Aarão, a quem escolhera.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 Mostraram entre eles os seus sinais e prodígios, na terra de Cão.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Mandou trevas, e a fez escurecer; e não foram rebeldes à sua palavra.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Converteu as suas águas em sangue, e matou os seus peixes.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 A sua terra produziu rãs em abundância, até nas câmaras dos seus reis.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Falou ele, e vieram enxames de moscas e piolhos em todo o seu termo.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Converteu as suas chuvas em saraiva, e fogo abrazador na sua terra.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Feriu as suas vinhas e os seus figueirais, e quebrou as árvores dos seus termos.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Falou ele, e vieram gafanhotos e pulgão sem número.
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 E comeram toda a erva da sua terra, e devoraram o fruto dos seus campos.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Feriu também a todos os primogênitos da sua terra, as primícias de todas as suas forças.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 E tirou-os para fora com prata e ouro, e entre as suas tribos não houve um só fraco.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 O Egito se alegrou quando eles sairam, porque o seu temor caira sobre eles.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Estendeu uma nuvem por coberta, e um fogo para alumiar de noite.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Oraram, e ele fez vir codornizes, e os fartou de pão do céu.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Abriu a penha, e dela correram águas; correram pelos lugares secos como um rio.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Porque se lembrou da sua santa palavra, e de Abraão, seu servo.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 E tirou dali o seu povo com alegria, e os seus escolhidos com regozijo.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 E deu-lhes as terras das nações; e herdaram o trabalho dos povos;
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Para que guardassem os seus preceitos, e observassem as suas leis. louvai ao Senhor.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Salmos 105 >