< 2 Samuel 22 >

1 E falou David ao Senhor as palavras deste cântico, no dia em que o Senhor o livrou das mãos de todos os seus inimigos e das mãos de Saul.
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 Disse pois: O Senhor é o meu rochedo, e o meu lugar forte, e o meu libertador.
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 Deus é o meu rochedo, nele confiarei: o meu escudo, e a força da minha salvação, o meu alto retiro, e o meu refúgio. O meu Salvador, de violência me salvaste.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 O Senhor, digno de louvor, invoquei, e de meus inimigos fiquei livre.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 Porque me cercaram as ondas de morte: as torrentes de Belial me assombraram.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 Cordas do inferno me cingiram; encontraram-me laços de morte. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
7 Estando em angústia, invoquei ao Senhor, e a meu Deus clamei: do seu templo ouviu ele a minha voz, e o meu clamor chegou aos seus ouvidos.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 Então se abalou e tremeu a terra, os fundamentos dos céus se moveram e abalaram, porque ele se irou.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 Subiu o fumo de seus narizes, e da sua boca um fogo devorador: carvões se incenderam dele.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 E abaixou os céus, e desceu: e uma escuridão havia debaixo de seus pés.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 E subiu sobre um cherubim, e voou: e foi visto sobre as asas do vento.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 E por tendas pôs as trevas ao redor de si: ajuntamento de águas, nuvens dos céus.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 Pelo resplendor da sua presença brasas de fogo se accendem.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 Trovejou desde os céus o Senhor: e o altíssimo fez soar a sua voz.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 E disparou flechas, e os dissipou: raios e os perturbou.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 E apareceram as profundezas do mar, os fundamentos do mundo se descobriram: pela repreensão do Senhor, pelo sopro do vento dos seus narizes.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 Desde o alto enviou, e me tomou: tirou-me das muitas águas.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 Livrou-me do meu possante inimigo, e daqueles que me tinham ódio, porque eram mais fortes do que eu.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 Encontraram-me no dia da minha calamidade: porém o Senhor se fez o meu esteio.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 E tirou-me à largura, e arrebatou-me dali; porque tinha prazer em mim.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 Recompensou-me o Senhor conforme à minha justiça: conforme à pureza de minhas mãos me retribuiu.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Porque guardei os caminhos do Senhor: e não me apartei impiamente do meu Deus.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 Porque todos os seus juízos estavam diante de mim: e de seus estatutos me não desviei.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 Porém fui sincero perante ele: e guardei-me da minha iniquidade.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 E me retribuiu o Senhor conforme à minha justiça, conforme à minha pureza diante dos seus olhos.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 Com o benigno te mostras benigno: com o varão sincero te mostras sincero.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 Com o puro te mostras puro: mas com o perverso te mostras avesso.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 E o povo aflito livras: mas teus olhos são contra os altivos, e tu os abaterás.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 Porque tu, Senhor, és a minha candeia: e o Senhor esclarece as minhas trevas.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 Porque contigo passo pelo meio dum esquadrão: pelo meu Deus salto um muro.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 O caminho de Deus é perfeito, e a palavra do Senhor refinada; e é o escudo de todos os que nele confiam.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 Porque, quem é Deus, senão o Senhor? e quem é rochedo, senão o nosso Deus?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 Deus é a minha fortaleza e a minha força, e ele perfeitamente desembaraça o meu caminho.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Faz ele os meus pés como os das cervas, e me põe sobre as minhas alturas.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 Instrui as minhas mãos para a peleja, de maneira que um arco de cobre se quebra pelos meus braços.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Também me deste o escudo da tua salvação, e pela tua brandura me vieste a engrandecer.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Alargaste os meus passos debaixo de mim, e não vacilaram os meus artelhos.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 Persegui os meus inimigos, e os derrotei, e nunca me tornei até que os consumisse.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 E os consumi, e os atravessei, de modo que nunca mais se levantaram, mas cairam debaixo dos meus pés.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Porque me cingiste de força para a peleja, fizeste abater-se debaixo de mim os que se levantaram contra mim.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 E deste-me o pescoço de meus inimigos, daqueles que me tinham ódio, e os destruí.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 Olharam, porém não houve libertador: sim, para o Senhor, porém não lhes respondeu.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 Então os moí como o pó da terra; como a lama das ruas os trilhei e dissipei.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Também me livraste das contendas do meu povo; guardaste-me para cabeça das nações; o povo que não conhecia me servirá.
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 Os filhos de estranhos se me sujeitaram; ouvindo a minha voz, me obedeceram.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 Os filhos de estranhos descairam; e, cingindo-se, sairam dos seus encerramentos.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 Vive o Senhor, e bendito seja o meu rochedo; e exaltado seja Deus, a rocha da minha salvação:
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 O Deus que me dá inteira vingança, e sujeita os povos debaixo de mim.
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 E o que me tira dentre os meus inimigos: e tu me exaltas sobre os que contra mim se levantam; do homem violento me livras.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Por isso, ó Senhor, te louvarei entre as gentes, e entoarei louvores ao teu nome.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Ele é a torre das salvações do seu rei, e usa de benignidade com o seu ungido, com David, e com a sua semente para sempre.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

< 2 Samuel 22 >