< Salmos 96 >

1 Cantae ao Senhor um cantico novo, cantae ao Senhor toda a terra.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Cantae ao Senhor, bemdizei o seu nome; annunciae a sua salvação de dia em dia.
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Annunciae entre as nações a sua gloria; entre todos os povos as suas maravilhas.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 Porque grande é o Senhor, e digno de louvor, mais tremendo do que todos os deuses.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Porque todos os deuses dos povos são idolos, mas o Senhor fez os céus.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Gloria e magestade estão ante a sua face, força e formosura no seu sanctuario.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Dae ao Senhor, ó familias dos povos, dae ao Senhor gloria e força.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Dae ao Senhor a gloria devida ao seu nome: trazei offerenda, e entrae nos seus atrios.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Adorae ao Senhor na belleza da sanctidade: tremei diante d'elle toda a terra.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Dizei entre as nações que o Senhor reina: o mundo tambem se firmará para que se não abale: julgará os povos com rectidão.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Alegrem-se os céus, e regozije-se a terra: brama o mar e a sua plenitude.
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 Alegre-se o campo com tudo o que ha n'elle: então se regozijarão todas as arvores do bosque,
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 Ante a face do Senhor, porque vem, porque vem a julgar a terra: julgará o mundo com justiça e os povos com a sua verdade.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.

< Salmos 96 >