< Salmos 94 >

1 Ó Senhor Deus, a quem a vingança pertence, ó Deus, a quem a vingança pertence, mostra-te resplandecente.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Exalta-te, tu, que és juiz da terra: dá a paga aos soberbos.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Até quando os impios, Senhor, até quando os impios saltarão de prazer?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 Até quando proferirão, e fallarão coisas duras, e se gloriarão todos os que obram a iniquidade?
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Reduzem a pedaços o teu povo, e affligem a tua herança.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Matam a viuva e o estrangeiro, e ao orphão tiram a vida.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Comtudo dizem: O Senhor não o verá; nem para isso attenderá o Deus de Jacob.
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Attendei, ó brutaes d'entre o povo; e vós, loucos, quando sereis sabios?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Aquelle que fez o ouvido não ouvirá? e o que formou o olho não verá?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Aquelle que argúe as gentes não castigará? e o que ensina ao homem o conhecimento não saberá?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 O Senhor conhece os pensamentos do homem, que são vaidade.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Bemaventurado é o homem aquem tu castigas, ó Senhor, e a quem ensinas a tua lei;
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 Para lhe dares descanço dos dias maus, até que se abra a cova para o impio.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Pois o Senhor não rejeitará o seu povo, nem desamparará a sua herança.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Mas o juizo voltará á rectidão, e seguil-o-hão todos os rectos do coração.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Quem será por mim contra os malfeitores? quem se porá por mim contra os que obram a iniquidade?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Se o Senhor não tivera ido em meu auxilio, a minha alma quasi que teria ficado no silencio.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Quando eu disse: O meu pé vacilla; a tua benignidade, Senhor, me susteve.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Na multidão dos meus pensamentos dentro de mim, as tuas consolações recrearam a minha alma.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Porventura o throno d'iniquidade te acompanha, o qual forja o mal por uma lei?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Elles se ajuntam contra a alma do justo, e condemnam o sangue innocente.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Mas o Senhor é a minha defeza; e o meu Deus é a rocha do meu refugio.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 E trará sobre elles a sua propria iniquidade; e os destruirá na sua propria malicia: o Senhor nosso Deus os destruirá.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Salmos 94 >