< Ezequiel 37 >

1 Veiu sobre mim a mão do Senhor, e o Senhor, pelo espirito, me levou e me poz no meio de um valle que estava cheio de ossos.
Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
2 E me fez passar por toda a roda d'elles; e eis que eram mui numerosos sobre a face do valle, e eis que estavam sequissimos.
Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
3 E me disse: Filho do homem, porventura viverão estes ossos? E eu disse: Senhor Jehovah, tu o sabes.
Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
4 Então me disse: Prophetiza sobre estes ossos, e dize-lhes: Ossos seccos, ouvi a palavra do Senhor.
Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
5 Assim diz o Senhor Jehovah a estes ossos: Eis que farei entrar em vós o espirito, e vivereis.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
6 E porei nervos sobre vós, e farei crescer carne sobre vós, e sobre vós estenderei pelle, e porei em vós o espirito, e vivereis, e sabereis que eu sou o Senhor.
Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
7 Então prophetizei como se me deu ordem; e houve um arroido, prophetizando eu; e eis que se fez um reboliço, e os ossos se achegaram, cada osso ao seu osso.
Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
8 E olhei, e eis que vinham nervos sobre elles, e cresceu a carne, e estendeu-se a pelle sobre elles por cima; porém não havia n'elles espirito.
Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
9 E elle me disse: Prophetiza ao espirito, prophetiza, ó filho do homem, e dize ao espirito: Assim diz o Senhor Jehovah: Vem dos quatro ventos, ó espirito, e assopra sobre estes mortos, e viverão.
Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
10 E prophetizei como elle me deu ordem: então o espirito entrou n'elles, e viveram, e se pozeram em seus pés, um exercito grande em extremo.
Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
11 Então me disse: Filho do homem, estes ossos são toda a casa de Israel: eis que dizem: Os nossos ossos se seccaram, e pereceu a nossa esperança: nós estamos cortados.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
12 Portanto prophetiza, e dize-lhes: Assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu abrirei as vossas sepulturas, e vos farei subir das vossas sepulturas, ó povo meu, e vos trarei á terra de Israel.
Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
13 E sabereis que eu sou o Senhor, quando eu abrir as vossas sepulturas, e vos fizer subir das vossas sepulturas, ó povo meu.
Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
14 E porei em vós o meu espirito, e vivereis, e vos metterei na vossa terra, e sabereis que eu, o Senhor, fallei isto, e o fiz, diz o Senhor.
Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
15 E veiu a mim a palavra do Senhor, dizendo:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Tu, pois, ó filho do homem, toma um pau, e escreve n'elle: A Judah e aos filhos de Israel, seus companheiros. E toma outro pau, e escreve n'elle: A José, o pau de Ephraim, e de toda a casa de Israel, seus companheiros.
“Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
17 E ajunta um ao outro, para que sejam um pau; e serão unidos na tua mão.
Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
18 E quando te fallarem os filhos do teu povo, dizendo: Porventura não nos declaras que significam estas coisas?
“In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
19 Então lhes dirás: Assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu tomarei o pau de José, que esteve na mão de Ephraim, e das tribus de Israel, seus companheiros, e os ajuntarei com elle ao pau de Judah, e farei d'elles um só pau, e elles se farão um só na minha mão.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
20 E os paus, sobre que houveres escripto, estarão na tua mão, perante os olhos d'elles.
Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
21 Dize-lhes pois: Assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu tomarei os filhos de Israel de entre as nações, para onde elles foram, e os congregarei de todas as partes, e os levarei á sua terra.
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
22 E d'elles farei uma nação na terra, nos montes d'Israel, e todos elles terão por seu rei um só rei; e nunca mais serão duas nações; nunca mais para o futuro se dividirão em dois reinos.
Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
23 E nunca mais se contaminarão com os seus idolos, nem com as suas abominações, nem com as suas prevaricações, e os livrarei de todas as suas habitações, em que peccaram, e os purificarei: assim me serão por povo, e eu lhes serei por Deus.
Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
24 E meu Servo David será rei sobre elles, e todos elles terão um só pastor; e andarão nos meus juizos, e guardarão os meus estatutos, e os farão.
“‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
25 E habitarão na terra que dei a meu servo Jacob, em que habitaram vossos paes; e habitarão n'ella, elles e seus filhos, e os filhos de seus filhos, para sempre, e David, meu servo, será seu principe eternamente.
Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
26 E farei com elles um concerto de paz; será com elles um concerto perpetuo; e os porei, e os multiplicarei, e porei o meu sanctuario no meio d'elles para sempre.
Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
27 E o meu tabernaculo estará com elles, e lhes serei por Deus e elles me serão por povo.
Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
28 E as nações saberão que eu sou o Senhor que sanctifico a Israel, quando estiver o meu sanctuario no meio d'elles para sempre.
Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”

< Ezequiel 37 >