< Amahubo 58 >
1 Isibili likhuluma okulungileyo yini, babusi? Lehlulela ngokuqonda yini, madodana abantu?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Yebo, enhliziyweni lenza okubi, lilinganisa udlakela lwezandla zenu emhlabeni.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 Ababi baba ngabemzini kusukela esiswini, bayaduha kusukela esizalweni, beqamba amanga.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Ubuhlungu babo bunjengobuhlungu benyoka, banjengebululu elingezwayo, elivimba indlebe yalo,
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 ukuze lingezwa ilizwi labalumbi abalumba amalumbo ngokuhlakanipha.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 Nkulunkulu, yephula amazinyo abo emlonyeni wabo, uphohloze amazinyo emihlathi yamabhongo ezilwane, Nkosi.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Kabancibilike njengamanzi agelezayo; nxa egobisa idandili lakhe ukutshoka umtshoko wakhe, babe njengabaqunywe iziqa.
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Kahambe njengomnenke oncibilikayo; njengomphunzo owesifazana, kabangaliboni ilanga.
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Imbiza zenu zingakaluzwa ukhuni lwameva, uzabaphephula esiphephweni njengabaphilayo njengentukuthelweni.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Olungileyo uzathokoza lapho ebona impindiselo, uzageza inyawo zakhe egazini lomubi.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Ukuze umuntu athi: Impela ukhona umvuzo wolungileyo; impela ukhona uNkulunkulu owahlulela emhlabeni.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”