< Izaga 25 >
1 Lalezi yizaga zikaSolomoni abantu bakaHezekhiya inkosi yakoJuda abazikopayo.
Waɗannan ƙarin karin maganar Solomon ne waɗanda mutanen Hezekiya sarkin Yahuda suka tara.
2 Kuludumo lukaNkulunkulu ukufihla udaba, kodwa kuludumo lwamakhosi ukuhlolisisa udaba.
Ɗaukakar Allah ce a ɓoye batun; a bayyana batun kuwa ɗaukakar sarakuna ne.
3 Amazulu ngokuphakama, lomhlaba ngokujula, lenhliziyo yamakhosi kakulakuhlolisiswa.
Kamar yadda sammai suna can bisa duniya kuma tana da zurfi, haka zukatan sarakuna suka wuce a bincika.
4 Susa amanyele esiliveni, besekuphuma isitsha somncibilikisi.
Ka tace azurfa sai kayan su fito don maƙerin azurfa;
5 Susa okhohlakeleyo phambi kwenkosi, besekuqiniswa isihlalo sayo sobukhosi ngokulunga.
ka cire mugaye daga gaban sarki, kursiyinsa kuwa zai kahu ta wurin adalci.
6 Ungaziqhenyi phambi kwenkosi, njalo ungemi endaweni yezikhulu;
Kada ka ɗaukaka kanka a gaban sarki, kada kuma ka nemi wa kanka wuri a cikin manyan mutane;
7 ngoba kungcono kuthiwe kuwe: Yenyukela ngapha, kulokuthi wehliswe phambi kwesiphathamandla, amehlo akho asibonileyo.
gara ya ce maka, “Ka hauro nan,” da a ƙasƙantar da kai a gaban wani mai makami. Abin da ka gani da idanunka
8 Ungaphangisi ukuphuma ukuyaphikisana, hlezi wenze ulutho ekucineni kwakho, lapho umakhelwane wakho esekuyangisile.
kada ka yi garaje kai ƙara a majalisa, gama me za ka yi a ƙarshe in maƙwabcinka ya ba ka kunya?
9 Mela udaba lwakho lomakhelwane wakho, kodwa ungavezi imfihlo yomunye;
In kai da maƙwabcinka kuka yi gardama, kada ka tona asirin wani,
10 hlezi okuzwayo akuyangise, lesigcono sakho singaphambuki.
in ba haka ba duk wanda ya ji zai kunyata ka ba za ka kuma taɓa rabuwa da wannan mummuna suna ba.
11 Ilizwi elikhulunywe ngokufaneleyo linjengama-apula egolide ezitsheni zesiliva ezibaziweyo.
Kalmar da aka faɗa daidai tana kamar zubin zinariyar da aka yi a mazubin azurfa.
12 Isongo legolide lesiceciso segolide elihle kungumkhuzi ohlakaniphileyo endlebeni ezwayo.
Kamar’yan kunnen zinariya ko kuwa kayan ado na zinariya zalla haka yake da tsawatawar mai hikima ga kunne mai saurarawa.
13 Isithunywa esithembekileyo kwabasithumileyo sinjengomqando weliqhwa elikhithikileyo ngosuku lokuvuna, ngoba sivuselela umphefumulo wamakhosi aso.
Kamar sanyin ƙanƙara a lokacin girbi haka ɗan saƙo mai aminci wanda aka aika; ya wartsakar da ran waɗanda suka aike shi.
14 Umuntu oziqhenya ngesipho samanga unjengamayezi lomoya okungelazulu.
Kamar gizagizai da kuma iska marar ruwan sama haka mutumin da yake fariya a kan kyautan da ba ya bayarwa.
15 Ngokubekezela umbusi angavunyiswa, lolimi oluthambileyo lwephula ithambo.
Ta wurin haƙuri akan rinjaye mai mulki, magana mai hankali kan karye ƙashi.
16 Utholile yini uluju? Dlana okwenele wena, hlezi uludle kakhulu, uluhlanze.
In ka sami zuma, ka sha isashe kawai, in ya yi yawa, za ka yi amai.
17 Unyawo lwakho kalungavami endlini kamakhelwane wakho, hlezi akusuthe akuzonde.
Kada ka cika ziyarar gidan maƙwabcinka yawan ganinka zai sa ya ƙi ka.
18 Umuntu ofakaza ubufakazi bamanga ngomakhelwane wakhe uyisagila lenkemba lomtshoko obukhali.
Kamar sanda ko takobi ko kibiya mai tsini haka yake da mutumin da yake ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinsa.
19 Ukuthemba ongathembekanga ngosuku lokuhlupheka kunjengezinyo elephukileyo, lonyawo olwenyeleyo.
Kamar haƙori mai ciwo ko yin tafiya da gurguwar ƙafa haka yake ga mai dogara da marasa aminci a lokacin wahala.
20 Ohlabelela izingoma enhliziyweni edabukileyo unjengokhupha isembatho ngosuku lwamakhaza, njengeviniga phakathi kwesoda.
Kamar wanda ya tuɓe riga a ranar da ake sanyi, ko kuwa kamar zuba ruwan tsami a kanwa, haka yake da mai rera waƙoƙi ga mai baƙin ciki.
21 Uba okuzondayo elambile, umnike isinkwa adle, njalo uba omile, umnike amanzi anathe;
In abokin gābanka yana jin yunwa, ka ba shi abinci ya ci; in yana jin ƙishi, ka ba shi ruwa ya sha.
22 ngoba uzabekelela amalahle omlilo ekhanda lakhe, leNkosi izakuvuza.
Ta yin haka, za ka tara garwashin wuta mai ci a kansa, Ubangiji kuma zai sāka maka.
23 Umoya wenyakatho uletha izulu, lolimi lwemfihlo ubuso obulolaka.
Kamar yadda iskar arewa kan kawo ruwan sama, haka jita-jita kan kawo fushi.
24 Kungcono ukuhlala engonsini yophahla kulalowesifazana wezinkani lendlini yokuhlanganyela.
Gara a zauna a kusurwar rufin ɗaki da a zauna a gida ɗaya da mace mai fitina.
25 Umbiko omuhle ovela elizweni elikhatshana unjengamanzi aqandayo emphefumulweni owomileyo.
Kamar ruwan sanyi ga ran da ya gaji haka yake da jin labari mai daɗi daga ƙasa mai nisa.
26 Olungileyo ozanyazanyiswayo phambi kokhohlakeleyo ungumthombo odungekileyo lesiphethu esonakeleyo.
Kamar rafi mai laka ko rijiyar da ta gurɓace haka yake da mai adalci wanda ya miƙa wuya ga mugaye.
27 Ukudla uluju olunengi kakulunganga; lokuthi badinge udumo lwabo kakusidumo.
Ba shi da kyau ka sha zuma da yawa, haka ma ba shi da kyau ka nemi girma wa kanka.
28 Umuntu ongathinti umoya wakhe unjengomuzi ofohlelweyo ongelamthangala.
Kamar birni da katangarsa sun rushe haka yake da mutumin da ba ya iya danne fushinsa.