< UMathewu 15 >
1 Kwasekufika kuJesu ababhali labaFarisi ababevela eJerusalema, bathi:
Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce,
2 Kungani abafundi bakho besephula isiko labadala? Ngoba kabagezi izandla zabo, nxa besidla isinkwa.
“Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”
3 Kodwa waphendula wathi kubo: Lani-ke kungani lisephula umlayo kaNkulunkulu ngenxa yesiko lenu?
Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku?
4 Ngoba uNkulunkulu walaya, wathi: Hlonipha uyihlo lonyoko; lokuthi: Othuka uyise kumbe unina kumele afe lokufa;
Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’
5 kodwa lina lithi: Loba ngubani othi kuyise kumbe kunina: Kungumnikelo, loba yini evela kimi ingakusiza,
Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’
6 njalo engasoze amhloniphe uyise kumbe unina; ngalokho lenza umlayo kaNkulunkulu ube yize ngenxa yesiko lenu.
ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku.
7 Bazenzisi, uIsaya waprofetha kuhle ngani, esithi:
Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,
8 Lababantu basondela kimi ngomlomo wabo, langendebe bangidumise; kodwa inhliziyo yabo ikhatshana lami.
“‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni, amma zukatansu suna nesa da ni.
9 Kodwa bangikhonza ngeze, befundisa izimfundiso eziyimilayo yabantu.
A banza suke mini sujada, koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’”
10 Esebizele kuye ixuku, wathi kilo: Lalelani futhi liqedisise.
Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane.
11 Kakusikho okungena emlonyeni okungcolisa umuntu; kodwa okuphuma emlonyeni, yikho okungcolisa umuntu.
Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”
12 Abafundi bakhe basebesondela bathi kuye: Uyazi yini ukuthi abaFarisi bathe ukulizwa lelilizwi bakhubeka?
Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”
13 Kodwa waphendula wathi: Sonke isihlahlakazana, uBaba osezulwini angasihlanyelanga, sizasitshunwa.
Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi.
14 Bayekeleni; bangabakhokheli beziphofu abayiziphofu; njalo nxa isiphofu sikhokhela isiphofu, zizawela emgodini zombili.
Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne. In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”
15 UPetro wasephendula wathi kuye: Sichasisele lumfanekiso.
Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”
16 UJesu wasesithi: Kanti lani lisengabangelakuqedisisa?
Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne?
17 Lilokhe lingaqedisisi yini, ukuthi konke okungena emlonyeni kuya esiswini, futhi kuyelahlelwa ngaphandle?
Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba?
18 Kodwa izinto eziphuma emlonyeni zivela enhliziyweni; lezi ziyamngcolisa umuntu.
Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum.
19 Ngoba enhliziyweni kuvela imicabango emibi, ukubulala, ubufebe, ukuphinga, ukweba, ukufakaza amanga, ukuhlambaza;
Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa.
20 yizo lezozinto ezimngcolisayo umuntu; kodwa ukudla ngezandla ezingagezwanga kakumngcolisi umuntu.
Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”
21 UJesu wasesuka lapho, waya kungxenye zeTire lezeSidoni.
Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon.
22 Njalo khangela, owesifazana ongumKhanani ovela kuleyomikhawulo, wakhala kuye esithi: Nkosi, Ndodana kaDavida, akungihawukele! Indodakazi yami ihlaselwe kubi lidimoni.
Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”
23 Kodwa kamphendulanga ngalizwi. Basebesondela kuye abafundi bakhe bamncenga, bathi: Mxotshe, ngoba uyakhala ngemva kwethu.
Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”
24 Kodwa waphendula wathi: Kangithunywanga, ngaphandle kuzo izimvu ezilahlekileyo zendlu yakoIsrayeli.
Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”
25 Kodwa weza wamkhonza wathi: Nkosi, ngisize.
Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”
26 Kodwa waphendula wathi: Kakukuhle ukuthatha isinkwa sabantwana, lokusiphosela izinjana.
Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”
27 Kodwa yena wathi: Yebo, Nkosi, kodwa lezinjana ziyadla okwemvuthuluka eziwa etafuleni labaninizo.
Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”
28 UJesu wasephendula wathi kuye: O mama, lukhulu ukholo lwakho! Kakube kuwe njengokuthanda kwakho. Indodakazi yakhe yasisila kusukela kulelohola.
Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.”’Yarta kuwa ta warke nan take.
29 UJesu wasesuka lapho weza eduzane kolwandle lweGalili; wenyukela entabeni wahlala phansi khona.
Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna.
30 Kwasekusiza kuye amaxuku amakhulu, beleziqhuli, iziphofu, izimungulu, izingini, labanye abanengi, basebebaphosela enyaweni zikaJesu, wasebasilisa;
Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su.
31 aze amangala amaxuku, ebona izimungulu zikhuluma, izingini ziphilile, iziqhuli zihamba, leziphofu zibona; basebemdumisa uNkulunkulu kaIsrayeli.
Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.
32 UJesu wasebizela kuye abafundi bakhe wathi: Ngilesihelo ngexuku, ngoba sebelami insuku ezintathu, bengelalutho lokudla; njalo kangithandi ukuthi ngibayekele bahambe bengadlanga, hlezi bayathe endleleni.
Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”
33 Abafundi bakhe basebesithi kuye: Sizazuza ngaphi enkangala izinkwa ezinengi kangaka, ukuthi zisuthise ixuku elikhulu kangaka?
Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”
34 UJesu wasesithi kubo: Lilezinkwa ezingaki? Basebesithi: Eziyisikhombisa, lenhlanzana ezinlutshwana.
Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?” Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da’yan ƙananan kifaye.”
35 Waselaya amaxuku ukuthi ahlale phansi emhlabathini.
Ya sa taron su zazzauna a ƙasa.
36 Wasethatha izinkwa eziyisikhombisa lenhlanzi, esebongile wazihlephula, wazinika abafundi bakhe, labafundi ixuku.
Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane.
37 Basebesidla bonke basutha; basebedobha imvuthu ezazisele, izitsha eziyisikhombisa zigcwele.
Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai.
38 Lalabo abadlayo babengamadoda azinkulungwane ezine, ngaphandle kwabesifazana labantwana.
Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara.
39 Eseyekele amaxuku ahamba wangena emkhunjini, weza emikhawulweni yeMagadala.
Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.