< UHezekheli 17 >

1 Ilizwi leNkosi laselifika kimi lisithi:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Ndodana yomuntu, yenza ilibho, ukhulume ngomfanekiso kuyo indlu yakoIsrayeli,
“Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
3 uthi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Ukhozi olukhulu, olukhulu ngempiko, olude ngezimpaphe, olugcwele insiba, olulemibalabala, lweza eLebhanoni, lwathatha isihloko somsedari,
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
4 lwaqunta isihloko sezingatshana zawo ezintsha, lwasisa elizweni lokuthengiselana, lwasibeka emzini wabathengisi.
ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
5 Lwaseluthatha okwenhlanyelo yalelolizwe, lwayifaka ensimini yenhlanyelo, lwayibeka ngasemanzini amanengi, lwayibeka njengomyezane.
“‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
6 Yasihluma, yaba livini elinabayo, elifitshane ngesithombo, ongatsha zalo zaphendukela kulo, lempande zalo zaba ngaphansi kwalo. Ngokunjalo laba livini, laveza ingatsha, lakhupha amahlumela.
ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
7 Kwasekusiba khona olunye ukhozi olukhulu, olukhulu ngempiko, lwande ngensiba. Khangela-ke, lelivini latshekisela impande zalo ngakulo, lakhuphela ingatsha zalo ngakulo, ukuze lulithelele ngemigelo yendawo yalo ehlanyelweyo.
“‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
8 Lalihlanyelwe ensimini enhle ngasemanzini amanengi ukuthi liveze ingatsha, lokuthi lithele isithelo, libe livini elihlekazi.
An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
9 Wothi: Itsho njalo iNkosi uJehova: Lizaphumelela yini? Kaluyikusiphuna yini impande zalo, luqume izithelo zalo, libune? Lizabuna kuwo wonke amahlamvu alo amatsha okumila kwalo, kungengengalo enkulu labantu abanengi, ukulisiphuna ngempande zalo.
“Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
10 Yebo, khangela, selihlanyelwe lizaphumelela yini? Kaliyikubuna ngokupheleleyo yini nxa umoya wempumalanga ulitshaya? Lizabunela ensimini yokumila kwalo.
Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
11 Laselifika ilizwi leNkosi kimi lisithi:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
12 Tshono khathesi kuyo indlu evukelayo: Kalazi yini ukuthi lezizinto ziyini? Uthi: Khangela, inkosi yeBhabhiloni yafika eJerusalema, yathatha inkosi yayo leziphathamandla zayo, yabaletha ngakuyo eBhabhiloni.
“Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
13 Yathatha owenzalo yesikhosini, yenza isivumelwano laye, yamngenisa phansi kwesifungo; yathatha abalamandla belizwe;
Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
14 ukuze umbuso ube phansi, ungaziphakamisi, ukuthi ngokulondoloza isivumelwano sakhe ume.
don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
15 Kodwa wayivukela ngokuthuma izithunywa zakhe eGibhithe, ukuze bamnike amabhiza labantu abanengi. Uzaphumelela yini? Owenza lezizinto uzaphepha yini? Kumbe angasephula isivumelwano aphephe yini?
Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
16 Kuphila kwami, itsho iNkosi uJehova, isibili endaweni yenkosi, embeka ukuthi abe yinkosi, osifungo sayo wasidelela, losivumelwano sayo wasephula, uzakufa layo phakathi kweBhabhiloni.
“‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
17 Njalo uFaro, lebutho elilamandla lexuku elikhulu, kayikumsiza empini ngokubuthelela idundulu langokwakha inqaba, ukuquma abantu abanengi.
Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
18 Ngoba edelele isifungo ngokwephula isivumelwano, lapho, khangela, esenikele isandla sakhe, wazenza zonke lezizinto, kayikuphunyuka.
Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
19 Ngakho, itsho njalo iNkosi uJehova: Kuphila kwami, isibili, isifungo sami asideleleyo, lesivumelwano sami asephulileyo, ngizakwehlisela phezu kwekhanda lakhe.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
20 Ngizakwendlala imbule lami phezu kwakhe, ukuthi abanjwe emjibileni wami, ngimlethe eBhabhiloni, ngimahlulele khonangesiphambeko sakhe aphambeke ngaso kimi.
Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
21 Labo bonke ababalekayo bakhe kanye lawo wonke amaviyo akhe bazakuwa ngenkemba, labaseleyo bazahlakazekela kuwo wonke umoya. Lizakwazi-ke ukuthi mina iNkosi ngikhulumile.
Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
22 Itsho njalo iNkosi uJehova: Lami ngizathatha esihlokweni somsedari omude, ngikumise. Ngizaqunta kuso isihloko sengatshana zawo ezintsha olubuthakathaka, mina ngiluhlanyele phezu kwentaba ende lephakemeyo.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
23 Entabeni yengqonga yakoIsrayeli ngizaluhlanyela; njalo luzakhupha ingatsha, luthele isithelo, lube ngumsedari omhlekazi; langaphansi kwawo kuzahlala yonke inyoni yophiko lonke; emthunzini wengatsha zawo zizahlala.
A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
24 Ngokunjalo zonke izihlahla zeganga zizakwazi ukuthi mina iNkosi ngithobisile isihlahla eside, ngaphakamisa isihlahla esifitshane, ngomisa isihlahla esiluhlaza, ngenza isihlahla esomileyo sihlume. Mina Nkosi ngikhulumile, ngakwenza.
Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”

< UHezekheli 17 >