< Ījaba 20 >

1 Tad Cofars no Naēmas atbildēja un sacīja:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Uz to manas sirds domas mani spiež atbildēt, un es nevaru valdīties.
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 Es dzirdu pārmācīšanu sev par kaunu, bet mans gars savā gudrībā zinās atbildēt.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Vai tu nezini, ka mūžam tā bijis, kamēr Dievs cilvēkus licis virs zemes,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 Ka bezdievīgo lielība ilgi nepastāv, un ka blēdnieka prieks paliek tik acumirkli?
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Jebšu viņa greznība uzkāptu līdz debesīm, un viņa galva sniegtu līdz padebešiem,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 Taču kā viņa sūds viņš mūžam zudīs; kas viņu redzējuši, tie sacīs: kur viņš ir?
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Viņš aizskries kā sapnis, ka to nevarēs atrast, un pazudīs kā parādīšana naktī.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 Acs, kas viņu redzējusi, to vairs neredzēs, un viņa vieta to vairs neieraudzīs.
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Viņa bērni pielabināsies pie nabagiem, un viņa roka dos atpakaļ viņa mantu.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Viņa kauli bija pilni jaunības spēka, bet apgulsies ar viņu pīšļos.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Jebšu blēdība bijusi salda viņa mutei, un viņš to slēpis apakš savas mēles,
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 Un viņš to mīlējis un nepametis, bet to paturējis savā mutē:
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Taču viņa barība pārvērtīsies viņa iekšās, par odžu žultīm tā būs iekš viņa.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Mantu, ko ierijis, viņš atkal izvems, un Dievs to izgrūdīs viņam no vēdera.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Odžu žultis viņš zīdīs, glodeņu dzelonis viņu nokaus.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Viņš neredzēs upes, kas ielejās tek no medus un piena.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Viņš gan strādās, bet to atdos un no tā nebaudīs; cik viņš arī neiemantos, prieka tam nebūs.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Jo viņš nospaidījis un atstājis nabagus, namus viņš laupījis, bet tos neuzcels.
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 Jo viņa kuņģis nebija pildāms, viņš neizglābsies caur savu mantu.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Viņa rīklei nekas neizmuka, tādēļ viņa labums nepastāvēs.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Pašā bagātā pilnībā viņam būs bēdas, visu apbēdināto roka nāks viņam virsū.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 Un notiks, lai viņa kuņģis top pilns, tad (Dievs) uz viņu sūtīs savas bardzības karstumu un uz viņu liks lītin līt, lai to rij.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 Viņš bēgs no dzelzs bruņām, un vara stops viņam izšaus cauri.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Viņš izvelk un no viņa miesām nāk ārā, no viņa žultīm spīdoša dzelzs, un nāves šausmas viņu pārņem.
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 Visāda tumsība apklās viņa krājumu, neuzpūsts uguns viņu aprīs, un nomaitās to atlikumu viņa dzīvoklī.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Debess viņa noziegumu darīs zināmu, un zeme celsies pret viņu.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Viņa nama krājums aizies, viņam izšķīdīs Dieva dusmības dienā.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Šī ir bezdievīga cilvēka daļa no Dieva, un viņa nospriesta mantība no tā stiprā Dieva.
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”

< Ījaba 20 >