< Pirmā Mozus 15 >

1 Pēc šīm lietām Tā Kunga vārds notika uz Ābramu iekš parādīšanās sacīdams: Nebīsties, Ābram; Es tev esmu par priekšturamām bruņām, un tava alga ir ļoti liela.
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 Tad Ābrams sacīja: Kungs, Dievs, ko Tu man dosi? Es aizeju bez bērniem un mana nama mantinieks ir šis Eliēzers no Damaskus.
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 Un Ābrams sacīja: redzi, man Tu neesi dzimumu devis, un redzi, manas saimes bērns būs mans mantinieks.
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 Un redzi, Tā Kunga vārds notika uz viņu sacīdams: šis nebūs tavs mantinieks, bet kas no tavām miesām nāks, tas būs tavs mantas ņēmējs.
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 Un Viņš to izveda ārā un sacīja: skaties uz debesīm un skaiti zvaigznes; vai tu tās vari izskaitīt? Un Viņš tam sacīja: tāpat būs tavs dzimums.
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 Un Ābrams ticēja uz To Kungu, un Viņš tam to pielīdzināja par taisnību.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 Un Viņš tam sacīja: Es esmu Tas Kungs, kas tevi izvedis no Ur iekš Kaldejas, ka tev dotu šo zemi iemantot.
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 Un tas sacīja: Kungs, Dievs, pie kam nopratīšu, ka es to iemantošu?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 Un Viņš tam sacīja: dabū Man treju gadu gotiņu un treju gadu kazu un treju gadu aunu un vienu ūbeli un vienu jaunu balodi.
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 Un tas Viņam dabūja visus tos un dalīja tos vidū uz pusēm un lika ikkatra daļu vienu pret otru, bet tos putnus viņš nedalīja.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 Un vanagi krita uz tām, un Ābrams tos nodzina.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 Un kad saule nogāja, tad Ābramam ciets miegs uznāca, un redzi, izbailes un liela tumsība tam uzkrita.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 Un Viņš sacīja uz Ābramu: zini zinādams, ka tavs dzimums piemitīs kādā zemē, kas tam nepieder, un tur viņus kalpinās un tiem grūti darīs četrsimt gadus.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 Bet to tautu, kam tie kalpos, Es arī sodīšu, un pēc tam tie izies ar lielu mantu.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 Un tu aiziesi pie saviem tēviem mierā un tapsi aprakts labā vecumā.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 Un ceturtā mūža augums nāks atkal šai vietā, jo Amoriešu netaisnība līdz šim vēl nav pilna.
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 Un notikās, kad saule nogāja un tumsa metās, tad redzi, dūmains ceplis un uguns liesma, kas cauri šāvās tiem upura gabaliem.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 Tanī dienā Tas Kungs cēla derību ar Ābramu, sacīdams: tavam dzimumam Es esmu devis šo zemi, no Ēģiptes upes līdz lielai Eifrat upei;
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 Keniešus un Ķenaziešus un Kadmoniešus,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 Hetiešus un Fereziešus un Refaīmiešus,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 Un Amoriešus un Kanaāniešus, Ģirgoziešus un Jebusiešus.
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”

< Pirmā Mozus 15 >