< 箴言 知恵の泉 28 >
1 惡者は逐ふ者なけれども逃げ 義者は獅子のごとくに勇まし
Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
2 國の罪によりて侯伯多くなり 智くして知識ある人によりて國は長く保つ
Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
3 弱者を虐ぐる貧人は糧をのこさざる暴しき雨のごとし
Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
4 律法を棄るものは惡者をほめ 律法を守る者はこれに敵す
Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
5 惡人は義きことを覺らず ヱホバを求むる者は凡の事をさとる
Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
7 律法を守る者は智子なり 放蕩なる者に交るものは父を辱かしむ
Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
8 利息と高利とをもてその財產を増すものは貧人をめぐむ者のために之をたくはふるなり
Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
9 耳をそむけて律法を聞ざる者はその祈すらも憎まる
In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
10 義者を惡き道に惑す者はみづから自己の阱に陷らん されど質直なる者は福祉をつぐべし
Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
11 富者はおのれの目に自らを智慧ある者となす されど聰明ある貧者は彼をはかり知る
Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
12 義者の喜ぶときは大なる榮あり 惡者の起るときは民身を匿す
Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
13 その罪を隱すものは榮ゆることなし 然ど認らはして之を離るる者は憐憫をうけん
Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
14 恒に畏るる人は幸福なり その心を剛愎にする者は災禍に陷るべし
Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
15 貧しき民を治むるあしき侯伯は吼る獅子あるひは饑たる熊のごとし
Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
16 智からざる君はおほく暴虐をおこなふ 不義の利を惡む者は遐齢をうべし
Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
17 人を殺してその血を心に負ふ者は墓に奔るなり 人これを阻むること勿れ
Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
18 義く行む者は救をえ 曲れる路に行む者は直に跌れん
Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
19 おのれの田地を耕す者は糧にあき 放蕩なる者に從ふものは貧乏に飽く
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
20 忠信なる人は多くの幸福をえ 速かに富を得んとする者は罪を免れず
Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
21 人を偏視るはよからず 人はただ一片のパンのために愆を犯すなり
Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
22 惡目をもつ者は財をえんとて急がはしく 却て貧窮のおのれに來るを知らず
Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
23 人を譴むる者は舌をもて諂ふ者よりも大なる感謝をうく
Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
24 父母の物を竊みて罪ならずといふ者は滅す者の友なり
Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
25 心に貧る者は爭端を起し ヱホバに倚賴むものは豊饒になるべし
Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
26 おのれの心を恃む者は愚なり 智慧をもて行む者は救をえん
Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
27 貧者に賙すものは乏しからず その目を掩ふ者は詛を受ること多し
Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
28 惡者の起るときは人匿れ その滅るときは義者ます
Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.