< Yohanna 9 >
1 Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
As he passed by, he saw a man blind from birth.
2 Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
His disciples asked him, “Rabbi, who sinned, this man or his parents, that he was born blind?”
3 Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
Jesus answered, “This man did not sin, nor did his parents, but that the works of God might be revealed in him.
4 Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
I must work the works of him who sent me while it is day. The night is coming, when no one can work.
5 Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
While I am in the world, I am the light of the world.”
6 Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
When he had said this, he spat on the ground, made mud with the saliva, anointed the blind man’s eyes with the mud,
7 Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
and said to him, “Go, wash in the pool of Siloam” (which means “Sent”). So he went away, washed, and came back seeing.
8 Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
Therefore the neighbors and those who saw that he was blind before said, “Is not this he who sat and begged?”
9 Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
Others were saying, “It is he.” Still others were saying, “He looks like him.” He said, “I am he.”
10 Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
They therefore were asking him, “How were your eyes opened?”
11 Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
He answered, “A man called Jesus made mud, anointed my eyes, and said to me, ‘Go to the pool of Siloam and wash.’ So I went away and washed, and I received sight.”
12 Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
Then they asked him, “Where is he?” He said, “I do not know.”
13 Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
They brought him who had been blind to the Pharisees.
14 A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
It was a Sabbath when Jesus made the mud and opened his eyes.
15 Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
Again therefore the Pharisees also asked him how he received his sight. He said to them, “He put mud on my eyes, I washed, and I see.”
16 Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
Some therefore of the Pharisees said, “This man is not from God, because he does not keep the Sabbath.” Others said, “How can a man who is a sinner do such signs?” So there was division among them.
17 Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
Therefore they asked the blind man again, “What do you say about him, because he opened your eyes?” He said, “He is a prophet.”
18 Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
The Jews therefore did not believe concerning him, that he had been blind and had received his sight, until they called the parents of him who had received his sight,
19 Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
and asked them, “Is this your son, whom you say was born blind? How then does he now see?”
20 Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
His parents answered them, “We know that this is our son, and that he was born blind;
21 Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
but how he now sees, we do not know; or who opened his eyes, we do not know. He is of age. Ask him. He will speak for himself.”
22 Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
His parents said these things because they feared the Jews; for the Jews had already agreed that if any man would confess him as Christ, he would be put out of the synagogue.
23 Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
Therefore his parents said, “He is of age. Ask him.”
24 Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
So they called the man who was blind a second time, and said to him, “Give glory to God. We know that this man is a sinner.”
25 Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
He therefore answered, “I do not know if he is a sinner. One thing I do know: that though I was blind, now I see.”
26 Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
They said to him again, “What did he do to you? How did he open your eyes?”
27 Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
He answered them, “I told you already, and you did not listen. Why do you want to hear it again? You do not also want to become his disciples, do you?”
28 Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
They insulted him and said, “You are his disciple, but we are disciples of Moses.
29 Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
We know that God has spoken to Moses. But as for this man, we do not know where he comes from.”
30 Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
The man answered them, “How amazing! You do not know where he comes from, yet he opened my eyes.
31 Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
We know that God does not listen to sinners, but if anyone is a worshiper of God and does his will, he listens to him.
32 Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn )
From the age (aiōn ) it has never been heard of that anyone opened the eyes of someone born blind.
33 In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
If this man were not from God, he could do nothing.”
34 Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
They answered him, “You were altogether born in sins, and do you teach us?” Then they threw him out.
35 Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
Jesus heard that they had thrown him out, and finding him, he said, “Do you believe in the Son of God?”
36 Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
He answered, “Who is he, Lord, that I may believe in him?”
37 Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
Jesus said to him, “You have both seen him, and it is he who speaks with you.”
38 Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
He said, “Lord, I believe!” and he worshiped him.
39 Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
Jesus said, “I came into this world for judgment, that those who do not see may see; and that those who see may become blind.”
40 Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
Those of the Pharisees who were with him heard these things, and said to him, “Are we also blind?”
41 Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.
Jesus said to them, “If you were blind, you would have no sin; but now you say, ‘We see.’ Therefore your sin remains.