< Ibraniyawa 1 >

1 A zamanin da, Allah ya yi wa kakanin kakanninmu magana ta hanyoyi ma su yawa iri iri, ta bakin annabawa.
In many parts and many ways, God, having spoken long ago to the fathers by the prophets,
2 Amma a zamanin nan na karshe, ya yi mana magana ta wurin Dansa, wanda ya sa magajin kome, wanda ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
in these last days speaks to us in [His] Son, whom He appointed heir of all things, through whom He also made the ages; (aiōn g165)
3 Shi ne hasken daukakar Allah, ainihin kamanin zatinsa. Ya na rike da dukkan abubuwa ta ikon kalmarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a hannun dama na madaukaki a can sama.
who being the brightness of the glory, and the impress of His subsistence, bearing up also all things by the saying of His might—having made a cleansing of our sins through Himself, sat down at the right hand of the Greatness in the highest,
4 Ta haka ya ke da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gada yake da fifiko nesa a kan nasu.
having become so much better than the messengers, as He inherited a more excellent name than them.
5 Domin kuwa wanene a cikin mala'iku Allah ya taba cewa, “Kai Da na ne, yau na zama Uba a gare ka?'' kuma, “Zan kasance Uba a gareshi, shi kuma, zai kasance Da a gare ni?''
For to which of the messengers did He ever say, “You are My Son—today I have begotten You?” And again, “I will be to Him for a Father, and He will be to Me for a Son?”
6 Kuma, da Allah ya kawo magaji a duniya, sai ya ce, “Dukan mala'ikun Allah su yi masa sujada.”
And when again He may bring the firstborn into the world, He says, “And let them worship Him—all messengers of God”;
7 A game da mala'iku kuma sai ya ce, “yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, masu hidimarsa kuma harsunan wuta.
and to the messengers, indeed, He says, “The [One] who is making His messengers spirits, and His ministers a flame of fire”;
8 A game da Dan, ya ce “kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne. Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. (aiōn g165)
but to the Son: “Your throne, O God, [is] throughout the age of the age; The scepter of righteousness [is the] scepter of Your kingdom; (aiōn g165)
9 Ka kaunaci aikin adalci, ka ki aikin sabo. Saboda haka Allah, wato Allahnka, ya shafe ka da man farin ciki fiye da tsararrakinka.”
You loved righteousness, and hated lawlessness; Because of this He anointed You—God, Your God—With oil of gladness above Your partners”;
10 “Tun farko, Ubangiji, kai ne ka hallici duniya. Sammai kuma aikin hannayenka ne.
and, “You, LORD, founded the earth at the beginning, And the heavens are a work of Your hands.
11 Za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufafi.
These will perish, but You remain, And all will become old as a garment,
12 Za ka nade su kamar mayafi, za su kuma sauya, amma kai kana nan ba sakewa, Har abada shekarunka ba za su kare ba.”
And You will roll them together as a mantle, and they will be changed, But You are the same, and Your years will not fail.”
13 Amma wanene a cikin mala'ikun Allah ya taba cewa, “Zauna a hannun dama na, sai na sa makiyanka a karkashin kafafunka?''
And to which of the messengers did He ever say, “Sit at My right hand, Until I may make Your enemies Your footstool?”
14 Ashe, ba dukkan mala'iku bane ruhohi, wadanda Allah yakan aika, don su yi wa wadanda za su gaji ceto hidima?
Are they not all spirits of service—being sent forth for ministry because of those about to inherit salvation?

< Ibraniyawa 1 >