< Zakariya 6 >

1 Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
And I turn back, and lift up my eyes, and look, and behold, four chariots are coming forth from between two of the mountains, and the mountains [are] mountains of bronze.
2 Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
In the first chariot [are] red horses, and in the second chariot brown horses,
3 ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
and in the third chariot white horses, and in the fourth chariot strong spotted horses.
4 Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
And I answer and say to the messenger who is speaking with me, “What [are] these, my lord?”
5 Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
And the messenger answers and says to me, “These [are] four spirits of the heavens coming forth from presenting themselves before the Lord of the whole earth.
6 Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
The brown horses that [are] therein, are coming forth to the land of the north; and the white have come forth to their back part; and the spotted have come forth to the land of the south;
7 Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
and the strong ones have come forth, and they seek to go to walk up and down in the earth”; and he says, “Go, walk up and down in the earth”; and they walk up and down in the earth.
8 Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
And he calls me, and speaks to me, saying, “See, those coming forth to the land of the north have caused My Spirit to rest in the land of the north.”
9 Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
And there is a word of YHWH to me, saying,
10 “Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
“Take of the captivity (who came from Babylon) from Heldai, from Tobijah, and from Jedaiah, and you have come in—you, in that day, indeed, you have come into the house of Josiah son of Zephaniah,
11 Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
and you have taken silver and gold, and have made a crown, and have placed [it] on the head of Joshua son of Josedech, the high priest,
12 Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
and have spoken to him, saying, Thus spoke YHWH of Hosts, saying, Behold, the Man! A Shoot—[is] His Name, And from His place He shoots up, And He has built the temple of YHWH.
13 Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
Indeed, He builds the temple of YHWH, And He carries away splendor, And He has sat and ruled on His throne, And has been a priest on His throne, And a counsel of peace is between both.
14 Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
And the crown is to Helem, and to Tobijah, and to Jedaiah, and to Hen son of Zephaniah, for a memorial in the temple of YHWH.
15 Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”
And the far-off come in, and they have built in the temple of YHWH, and you have known that YHWH of Hosts has sent me to you, indeed, it has come to pass, if you certainly listen to the voice of your God YHWH.”

< Zakariya 6 >