< Zakariya 12 >

1 Annabci, maganar Ubangiji game da Isra’ila. Ubangiji, wanda ya shimfiɗa sammai, wanda ya kafa harsashin duniya, wanda kuma ya yi ruhun mutum a cikinsa ya ce,
»Breme o Gospodovi besedi za Izrael, « govori Gospod, ki razprostira nebo in polaga temelj zemlji in oblikuje človeškega duha znotraj njega.
2 “Zan sa Urushalima ta zama kwaf mai sa mutanen da suke a dukan kewayenta, jiri. Yaƙi zai kewaye Urushalima har yă shafi Yahuda ma.
»Glej, Jeruzalem bom naredil čašo trepetanja vsemu ljudstvu naokoli, ko bodo v obleganju tako zoper Juda in zoper Jeruzalem.
3 A ranan nan, sa’ad da duk al’umman duniya za su tayar mata, zan sa Urushalima ta zama dutsen da ba a iya matsarwa ga dukan al’ummai. Duk waɗanda suka yi ƙoƙari su matsar da shi za su ji ciwo.
Na tisti dan bom naredil [prestolnico] Jeruzalem obremenilni kamen za vse ljudstvo. Vsi, ki se bremenijo s tem, bodo razsekani na koščke, čeprav bo vse ljudstvo zemlje zbrano zoper njo.
4 A ranan nan zan sa kowane doki yă tsorata, mai hawan dokin kuma yă haukace,” in ji Ubangiji. “Zan sa idanuna in tsare gidan Yahuda, amma zan makantar da dukan dawakan al’ummai.
Na tisti dan, « govori Gospod, »bom vsakega konja udaril z osuplostjo in njegovega jezdeca z norostjo in svoje oči bom odprl nad Judovo hišo in vsakega konja ljudstva bom udaril s slepoto.
5 Sa’an nan shugabannin Yahuda za su ce a cikin zukatansu, ‘Mutanen Urushalima suna da ƙarfi domin Ubangiji Maɗaukaki shi ne Allahnsu.’
Voditelji Juda bodo v svojem srcu rekli: ›Prebivalci Jeruzalema bodo moja moč v Gospodu nad bojevniki, njihovem Bogu.‹
6 “A ranan nan zan sa shugabannin Yahuda su zama kamar tukunyar wuta a tarin itacen wuta; kamar harshen wuta a dammunan hatsi. Za su ƙone dukan mutanen da suke kewaye da su hagu da dama, amma babu abin da zai taɓa mutanen Urushalima.
Na tisti dan bom naredil voditelje Juda kakor ognjeno ognjišče med lesom in ognjeno baklo v snopu in použili bodo vse ljudstvo naokoli, na desni roki in na levi in Jeruzalem bo ponovno naseljen na svojem lastnem kraju, celó v Jeruzalemu.
7 “Ubangiji zai ceci wuraren zaman Yahuda da farko, don kada darajar gidan Dawuda da mazaunan Urushalima su fi na Yahuda daraja.
Gospod bo tudi najprej rešil Judove šotore, da se slava Davidove hiše in slava prebivalcev Jeruzalema ne bo poveličevala zoper Juda.
8 A ranan nan Ubangiji zai kiyaye waɗanda suke zama a Urushalima, domin marasa ƙarfi a cikinsu su zama kamar Dawuda, gidan Dawuda kuma zai zama kamar Allah, kamar mala’ikan Ubangiji da yake tafiya a gabansu.
Na tisti dan bo Gospod branil prebivalce Jeruzalema. Kdor bo na tisti dan med njimi slaboten, bo kakor David in Davidova hiša bo kakor Bog, kakor Gospodov angel pred njimi.
9 A ranan nan zan fito don in hallaka dukan al’umman da suka yaƙi Urushalima.
In zgodilo se bo na tisti dan, da si bom prizadeval uničiti vse narode, ki pridejo zoper Jeruzalem.
10 “Zan kuma zubo wa gidan Dawuda da mazaunan Urushalima ruhun alheri da na addu’a. Za su dube ni, wannan da suka soke shi, za su kuma yi makoki dominsa kamar yadda mutum yakan yi makokin mutuwar ɗansa tilo, su kuma yi baƙin ciki ƙwarai kamar yadda mutum yakan yi baƙin ciki don ɗan fari.
Na Davidovo hišo in na prebivalce Jeruzalema bom izlil duha milosti in ponižnih prošenj in gledali bodo name, ki so ga prebodli in žalovali bodo za njim, kakor nekdo žaluje za svojim edinim sinom in v grenkobi bodo za njim, kakor nekdo, ki je v grenkobi zaradi svojega prvorojenca.
11 A ranan nan kuka a Urushalima zai yi yawa kamar kukan Hadad Rimmon a filin Megiddo.
Na tisti dan bo v Jeruzalemu veliko žalovanje, kakor žalovanje za Hadád Rimónom v dolini Megído.
12 Ƙasar za tă yi makoki, kowane iyali zai yi makoki a ware, tare da matansu su ma a ware, iyalin gidan Dawuda da matansu, iyalin gidan Natan da matansu,
Dežela bo žalovala, vsaka družina posebej; družina Davidove hiše posebej in njihove žene posebej, družina Natánove hiše posebej in njihove žene posebej,
13 iyalin gidan Lawi da matansu, iyalin gidan Shimeyi da matansu,
družina Lévijeve hiše posebej in njihove žene posebej, Šimíjeva družina posebej in njihove žene posebej.
14 dukan sauran iyalan kuma da matansu.
Vse družine, ki preostanejo, vsaka družina posebej in njihove žene posebej.«

< Zakariya 12 >