< Zakariya 1 >

1 A wata na bakwai na shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
In the eighth month, in the second year of Darius, a word of YHWH has been to Zechariah, son of Berechiah, son of Iddo the prophet, saying,
2 “Ubangiji ya yi fushi sosai da kakanninku.
“YHWH was angry against your fathers—wrath!
3 Saboda haka ka gaya wa mutanen, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku komo gare ni,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘ni kuma zan komo gare ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
And you have said to them, Thus said YHWH of Hosts: Return to Me, A declaration of YHWH of Hosts, And I return to you, said YHWH of Hosts.
4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka ce musu, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku juya daga mugayen hanyoyinku da mugayen abubuwan da kuke yi.’ Amma ba su saurara ba, ko ma su kula da ni, in ji Ubangiji.
You will not be as your fathers, To whom the former prophets called, Saying, Thus said YHWH of Hosts: Please turn back from your evil ways and from your evil doings, And they did not listen, Nor attend to Me—a declaration of YHWH.
5 Yanzu ina kakanninku suke? Annabawan kuma fa, sun rayu har abada ne?
Your fathers—where [are] they? And the prophets—do they live for all time?
6 Amma maganata da dokokina da na umarta ta wurin bayina annabawa fa, ashe, ba su tabbata ba a kan kakanninku? “Sa’an nan suka tuba suka ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki ya yi mana daidai abin da hanyoyinmu suka cancanci mu samu, kamar dai yadda ya yi niyya yi.’”
Only, My words and My statutes, That I commanded My servants the prophets, Have they not overtaken your fathers? And they turn back and say: As YHWH of Hosts designed to do to us, According to our ways, and according to our doings, So He has done to us.”
7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato, watan Shebat, a shekara ta biyu ta Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Zakariya ɗan Berekiya ɗan Iddo.
On the twenty-fourth day of the eleventh month (it [is] the month of Sebat), in the second year of Darius, a word of YHWH has been to Zechariah, son of Berechiah, son of Iddo the prophet. [He was] saying:
8 Da dare, na ga wahayi, a gabana kuwa ga mutum a kan jan doki! Yana tsaye a cikin itatuwa masu furanni, a bayansa a cikin itatuwan ci-zaƙi, a bayansa kuwa akwai dawakai masu ruwan ja, ruwan ƙasa-ƙasa da kuma ruwan fari.
I have seen by night, and behold, one riding on a red horse, and he is standing between the myrtles that [are] in the shade, and behind him [are] horses, red, bay, and white.
9 Sai na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan ranka yă daɗe?” Mala’ikan da yake magana da ni ya amsa ya ce, “Zan nuna maka mene ne su.”
And I say, “What [are] these, my lord?” And the messenger who is speaking with me says to me, “I show you what these [are].”
10 Sai mutumin da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin ya yi bayani cewa, “Su ne waɗanda Ubangiji ya aika ko’ina a duniya.”
And the one who is standing between the myrtles answers and says, “These [are] they whom YHWH has sent to walk up and down in the land.”
11 Sai suka ce wa mala’ikan da yake tsaye cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun ratsa ko’ina a duniya, sai muka ga duniya duka tana zaman lafiya.”
And they answer the Messenger of YHWH who is standing between the myrtles, and say, “We have walked up and down in the land, and behold, all the land is sitting still, and at rest.”
12 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Maɗaukaki, har yaushe za ka ci gaba da ƙi nuna wa Urushalima da kuma garuruwan Yahuda jinƙai, waɗanda kake fushi da su shekarun nan saba’in?”
And the Messenger of YHWH answers and says, “YHWH of Hosts! Until when do You not pity Jerusalem, and the cities of Judah, that You have abhorred these seventy years?”
13 Sai Ubangiji ya yi wa mala’ikan da ya yi magana da ni magana da kalmomi masu daɗi da kuma masu ta’azantarwa.
And YHWH answers the messenger, who is speaking with me, good words, comfortable words.
14 Sai mala’ikan da yake magana da ni ya ce, “Ka yi shelar maganan nan, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ina kishi domin Urushalima da Sihiyona,
And the messenger who is speaking with me, says to me, “Call, saying, Thus said YHWH of Hosts: I have been zealous for Jerusalem, And for Zion [with] great zeal.
15 amma ina fushi da ƙasashen da suke ji suna zaman lafiya, na ɗan yi fushina kawai, amma sai suka ƙara musu masifar.’
And [with] great wrath I am angry against the nations who are at ease, For I was a little angry, and they assisted—for evil.
16 “Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Zan komo Urushalima da jinƙai, a can ne za a sāke gina gidana. Za a kuma miƙe ma’auni a bisa Urushalima,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore, thus said YHWH: I have turned to Jerusalem with mercies, My house is built in it, A declaration of YHWH of Hosts, And a line is stretched over Jerusalem.
17 “Ci gaba da yin shela, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Garuruwana za su sāke kwarara da wadata, Ubangiji kuma zai sāke yi wa Sihiyona ta’aziyya, yă kuma zaɓi Urushalima.’”
Again call, saying, Thus said YHWH of Hosts: Again My cities overflow from good, And YHWH has again comforted Zion, And He has fixed again on Jerusalem.”
18 Sa’an nan na dubi sama a gabana kuwa sai ga ƙahoni huɗu!
And I lift up my eyes, and look, and behold, four horns.
19 Na tambayi mala’ikan da yake mini magana, na ce, “Mene ne waɗannan?” Ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda, Isra’ila da kuma Urushalima.”
And I say to the messenger who is speaking with me, “What [are] these?” And he says to me, “These [are] the horns that have scattered Judah, Israel, and Jerusalem.”
20 Sa’an nan Ubangiji ya nuna mini maƙera guda huɗu.
And YHWH shows me four artisans.
21 Na yi tambaya na ce, “Mene ne waɗannan suke zuwa yi?” Ya amsa ya ce, “Waɗannan ne ƙahonin da suka watsar da Yahuda har ba wanda yake iya ɗaga kansa, amma maƙeran sun zo don su tsorata su su kuma saukar da ƙahonin ƙasashen nan waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuda don su warwatsa ta.”
And I say, “What [are] these coming to do?” And He speaks, saying, “These [are] the horns that have scattered Judah, so that no one has lifted up his head, and these come to trouble them, to cast down the horns of the nations who are lifting up a horn against the land of Judah—to scatter it.”

< Zakariya 1 >