< Titus 1 >
1 Bulus, bawan Allah da kuma manzon Yesu Kiristi saboda bangaskiyar zaɓaɓɓu na Allah da kuma sanin gaskiya wadda take kaiwa ga rayuwa ta tsoron Allah
Pavel, služebník Boží, apoštol pak Ježíše Krista, podlé víry vyvolených Božích, a známosti pravdy, kteráž jest podlé pobožnosti,
2 duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, (aiōnios )
K naději života věčného, kterýž zaslíbil před časy věků ten, kterýž nikdy neklamá, Bůh, (aiōnios )
3 da lokacin da Allah ya zaɓa ya cika sai ya bayyana maganarsa a sarari ta wurin wa’azin da aka danƙa mini amana ta wurin umarnin Allah Mai Cetonmu,
Zjevil pak časy svými to slovo své, skrze kázaní mně svěřené, podlé zřízení spasitele našeho Boha,
4 Zuwa ga Titus, ɗana na gaske a tarayyarmu cikin bangaskiya. Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Kiristi Yesu Mai Cetonmu, su kasance tare da kai.
Titovi, vlastnímu synu u víře obecné: Milost, milosrdenství a pokoj od Boha Otce a Pána Jezukrista spasitele našeho.
5 Dalilin da ya sa na bar ka a Kirit shi ne don ka daidaita abubuwan da suka rage da ba a kammala ba, ka kuma naɗa dattawa a kowane gari, yadda na umarce ka.
Z té příčiny zanechal jsem tebe v Krétě, abys to, čehož tam ještě potřebí, spravil, a ustanovil po městech starší, jakož i já při tobě jsem zřídil,
6 Dole dattijo yă kasance marar aibi, mijin mace guda, mutumin da’ya’yansa masu bi ne, waɗanda kuma ba a san su da lalata ko rashin biyayya ba.
Jest-li kdo bez úhony, jedné manželky muž, dítky maje věřící, na kteréž by nemohlo touženo býti, že by byli bůjní, aneb nepoddaní.
7 Da yake an danƙa wa mai kula da ikkilisiya riƙon amana saboda Allah, dole yă zama marar aibi ba mai girman kai ba, ba mai saurin fushi ba, ba mai buguwa ba, ba mai rikici ba, ba kuma mai son ƙazamar riba ba.
Neboť biskup má býti bez úhony, jako Boží šafář, ne svémyslný, ne hněvivý, ne piján vína, ne bitec, ne žádostivý mrzkého zisku,
8 A maimakon haka dole yă zama mai karɓan baƙi, mai son abu nagari, mai kamunkai, mai adalci, mai tsarki da kuma natsattse.
Ale přívětivý k hostem, milovník dobrých, opatrný, spravedlivý, svatý, zdrželivý,
9 Dole yă riƙe tabbataccen saƙon nan kam-kam yadda aka koyar, don yă iya ƙarfafa waɗansu da sahihiyar koyarwa yă kuma ƙaryata waɗanda suke gāba da shi.
Pilně se přídržící věrné řeči k vyučování dostatečné, aby mohl i napomínati učením zdravým, i ty, kteříž odpírají, přemáhati.
10 Gama akwai’yan tawaye da yawa, masu surutun banza da masu ruɗi, musamman ƙungiyar masu kaciya.
Neboť jsou mnozí nepoddaní, marnomluvní, i svůdcové myslí, zvláště ti, kteříž jsou z obřízky.
11 Dole a hana su yin magana, domin suna kawo rushewar iyalai ta wurin koyar da abubuwan da bai kamata su koyar ba don neman ƙazamar riba.
Jimž musejí ústa zacpána býti; kteříž celé domy převracejí, učíce neslušným věcem, pro mrzký zisk.
12 Wani daga cikin annabawansu ma ya ce, “Kiretawa a kullum maƙaryata ne, mugayen dabbobi, ragwaye haɗamammu.”
Řekl jeden z nich, vlastní jejich prorok: Kretenští jsou vždycky lháři, zlá hovada, břicha lenivá.
13 Wannan shaida gaskiya ce. Saboda haka, sai ka tsawata musu sosai, don su zama sahihai a wajen bangaskiya,
Svědectví to pravé jest. A protož tresciž je přísně, ať jsou zdraví u víře,
14 ba za su kuma mai da hankalinsu ga tatsuniyoyin Yahudawa ko ga umarnan waɗanda suke ƙin gaskiya ba.
Nešetříce Židovských básní a přikázaní lidí těch, kteříž se odvracují od pravdy.
15 Ga tsarkaka kuwa, kome mai tsarki ne, amma ga waɗanda suke marasa tsarki da kuma marasa ba da gaskiya, ba abin da yake da tsarki. Gaskiya dai, hankulansu da lamirinsu duk marasa tsarki ne.
Všecko zajisté čisté jest čistým, poškvrněným pak a nevěřícím nic není čistého, ale poškvrněna jest i mysl jejich i svědomí.
16 Sun ɗauka cewa sun san Allah, amma ta wurin ayyukansu suna mūsunsa. Sun zama abin ƙyama, marasa biyayya, ba su ma isa su yi aiki nagari ba.
Vypravují o tom, že Boha znají, ale skutky svými toho zapírají, ohavní jsouce, a nepoddaní, a ke všelikému skutku dobrému nehodní.