< Waƙar Waƙoƙi 4 >

1 Ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata! Kai, ke kyakkyawa ce! Idanunki sun yi kamar na kurciya a cikin lulluɓinki. Gashinki ya yi kamar garken awaki da suke gangarawa daga Dutsen Gileyad.
Behold, thou art beautiful, my beloved, behold, thou art beautiful: thy dovelike eyes [look forth] from behind thy vail; thy hair is like a flock of goats, that come quietly down from Mount Gil'ad.
2 Haƙoranki sun yi kamar garken tumakin da ba a daɗe da yin musu sausaya ba, da suke haurawa daga inda aka yi musu wanka. Kowanne yana tare da ɗan’uwansa; babu waninsu da yake shi kaɗai.
Thy teeth are like a flock of well-selected sheep, which are come up from the washing, all of which bear twins, and there is not one among them that is deprived of her young.
3 Leɓunanki kamar zaren jan garura bakinki yana da kyau. Kumatunki sun yi kamar rumman da aka tsaga biyu a cikin lulluɓinki.
Like a thread of scarlet are thy lips, and thy mouth is comely: like the half of a pomegranate is the upper part of thy cheek behind thy vail.
4 Wuyanki ya yi kamar hasumiyar Dawuda, da aka gina da daraja; a kansa an rataye garkuwoyi dubu, dukansu garkuwoyin jarumawa ne.
Thy neck is like the tower of David built on terraces, a thousand shields hang-thereon, all the quivers of the mighty men.
5 Nonanki biyu sun yi kamar bareyi biyu, kamar tagwayen barewa da suke kiwo a cikin furen bi-rana.
Thy two breasts are like two fawns, the twins of the roe, that feed among the lilies.
6 Sai gari ya waye inuwa kuma ta watse, zan je dutsen mur da kuma tudun turare.
Until the day became cool, and the shadows flee away, will I get me to the mountain of myrrh, and to the hill of frankincense.
7 Duk, ke kyakkyawa ce, ƙaunatacciyata; babu wani lahani a cikinki.
Thou art altogether beautiful, my beloved, and there is no blemish on thee.—
8 Ki tare da ni daga Lebanon, amaryata, zo tare da ni daga Lebanon. Ki gangara daga ƙwanƙolin Amana, daga ƙwanƙolin Senir, ƙwanƙolin Hermon, daga ramin zaki da kuma dutsen da damisoshi suke zama.
Come with me from Lebanon, O bride, with me from Lebanon: look about from the top of Amanah, from the top of Senir and Chermon, from the lions' dens, from the leopards' mountains.
9 Kin saci zuciyata,’yar’uwata, amaryata; kin saci zuciyata da hararar idanunki, da dutse mai daraja guda na abin wuyanki.
Thou hast ravished my heart, O my sister, [my] bride; thou hast ravished my heart with one of thy eyes, with one chain of thy neck.
10 Ƙaunarki abar farin ciki ne,’yar’uwata, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi gamsuwa, ƙanshin turarenki kuma ya fi duk wani kayan yaji!
How beautiful are thy caresses, O my sister, [my] bride! how much more pleasant are thy caresses than wine! and the smell of thy fragrant oils more than all spices.
11 Leɓunanki suna zub da zaƙi kamar kakin zuma, amaryata; madara da zuma suna a ƙarƙashin harshenki. Ƙanshin rigunanki ya yi kamar na Lebanon.
Of sweet honey drop thy lips, O bride: honey and milk are under thy tongue; and the scent of thy garments is like the scent of Lebanon.
12 Ke lambu ne da aka kulle,’yar’uwata, amaryata; ke maɓulɓula ce da aka kewaye, maɓulɓular da aka rufe.
A locked-up garden is my sister, [my] bride; a locked-up spring, a sealed fountain.
13 Shuke-shukenki gonar rumman ne da’ya’yan itace masu kyau na lalle da nardi,
Thy sprouts are an orchard of pomegranates, with precious fruits, copher and spikenard;
14 nardi, da asfaran, kalamus, da kirfa, da kowane irin itacen turare, da mur da aloyes da kuma dukan kayan yaji masu kyau.
Spikenard and saffron; calamus and cinnamon, with all the trees of frankincense; myrrh and aloes, with all the chief of spices;
15 Ke lambun maɓulɓula ne, rijiya mai ruwan da yake gudu yana gangarawa daga Lebanon.
A garden-spring, a well of living waters, and flowing down from Lebanon.—
16 Farka, iskar arewa, ki kuma zo, iskar kudu! Hura a kan lambuna, don ƙanshinsa yă bazu har waje. Bari ƙaunataccena yă zo cikin lambunsa yă ɗanɗana’ya’yan itacensa mafi kyau.
Awake, O north wind; and come thou, O south; blow over my garden, that its spices may flow out. Let my friend come into his garden, and eat its precious fruits.—

< Waƙar Waƙoƙi 4 >