< Rut 1 >

1 A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
And it comes to pass, in [the] days [when] the ones judging judge, that there is a famine in the land, and there goes a man from Beth-Lehem-Judah to sojourn in the fields of Moab, he, and his wife, and his two sons.
2 Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
And the name of the man [is] Elimelech, and the name of his wife Naomi, and the name of his two sons Mahlon and Chilion, Ephraimites from Beth-Lehem-Judah; and they come into the fields of Moab, and are there.
3 To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da’ya’yanta maza biyu.
And Elimelech husband of Naomi dies, and she is left, she and her two sons;
4 Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
and they take to them wives, Moabitesses: the name of the first [is] Orpah, and the name of the second Ruth; and they dwell there about ten years.
5 sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
And they die also, both of them—Mahlon and Chilion—and the woman is left of her two children and of her husband.
6 Sa’ad da ta ji a Mowab cewa Ubangiji ya zo don yă taimaki mutanensa ta wurin tanada musu da abinci, sai Na’omi tare da surukanta suka shirya su koma gida daga can.
And she rises, she and her daughters-in-law, and turns back from the fields of Moab, for she has heard in the fields of Moab that God has looked after His people—to give to them bread.
7 Tare da surukanta biyu suka bar inda suka zauna suka kuma kama hanya da za tă komar da su zuwa ƙasar Yahuda.
And she goes out from the place where she has been, and her two daughters-in-law with her, and they go in the way to return to the land of Judah.
8 Sai Na’omi ta ce wa surukanta biyu, “Ku koma, kowannenku, zuwa gidan mahaifiyarta. Bari Ubangiji yă nuna muku alheri yadda kuka nuna wa matattun nan da kuma gare ni.
And Naomi says to her two daughters-in-law, “Go, return, each to the house of her mother; YHWH does with you kindness as you have done with the dead, and with me;
9 Bari Ubangiji yă sa kowannenku ta sami hutu a gidan wani miji.” Sa’an nan ta sumbace su suka kuma yi kuka da ƙarfi
YHWH grants to you, and you find rest each in the house of her husband”; and she kisses them, and they lift up their voice and weep.
10 suka ce mata, “Za mu tafi tare da ke zuwa ga mutanenki.”
And they say to her, “Surely with you we go back to your people.”
11 Amma Na’omi ta ce, “Ku koma gida,’ya’yana mata. Don me za ku tafi tare da ni? Zan ƙara samun waɗansu’ya’ya maza da za su zama mazanku ne?
And Naomi says, “Turn back, my daughters; why do you go with me? Are there yet to me sons in my bowels that they have been to you for husbands?
12 Ku koma gida’ya’yana mata; na tsufa ainun da zan sāke samun wani miji. Ko ma na yi tsammani har yanzu ina da bege, ko ma na sami miji a wannan dare na kuma haifi’ya’ya maza,
Turn back, my daughters, go, for I am too aged to be to a husband; though I had said, There is for me hope, also, I have been tonight to a husband, and also I have borne sons:
13 za ku jira sai sun yi girma? Za ku ci gaba da kasance babu aure saboda su? A’a,’ya’yana mata. Ina da baƙin ciki ƙwarai fiye da ku, domin hannun Ubangiji ya yi gāba da ni!”
do you wait for them until they grow up? Do you shut yourselves up for them, not to be to a husband? No, my daughters, for more bitter to me than to you, for the hand of YHWH has gone out against me.”
14 A kan wannan suka sāke ɓarke da kuka. Sa’an nan Orfa ta sumbaci surukarta ta yi bankwana, amma Rut ta manne mata.
And they lift up their voice, and weep again, and Orpah kisses her mother-in-law, and Ruth has cleaved to her.
15 Sai Na’omi ta ce, “Duba,’yar’uwanki ta koma zuwa ga mutanenta da kuma allolinta. Ki koma tare da ita.”
And she says, “Behold, your sister-in-law has turned back to her people, and to her god, turn back after your sister-in-law.”
16 Rut Amma Rut ta amsa, “Kada ki roƙe ni in bar ki ko in koma daga gare ki. Inda za ki, zan tafi, kuma inda za ki zauna, zan zauna. Mutanenki, za su zama mutanena kuma Allahnki, zai zama Allahna.
And Ruth says, “Do not urge me to leave you—to turn back from after you; for to where you go I go, and where you lodge I lodge; your people [is] my people, and your God my God.
17 Inda za ki mutu zan mutu, zan mutu a can kuma za a binne ni. Bari Ubangiji ya hukunta ni da tsanani sosai, in wani abu in ba mutuwa ce ta raba ke da ni ba.”
Where you die I die, and there I am buried; thus does YHWH to me, and thus He adds—for death itself parts between me and you.”
18 Sa’ad da Na’omi ta gane cewa Rut ta ƙudura tă tafi tare da ita, sai ta daina nema tă koma.
And she sees that she is strengthening herself to go with her, and she ceases to speak to her;
19 Saboda haka matan biyu suka ci gaba da tafiya sai da suka isa Betlehem. Da suka isa Betlehem, sai dukan garin ya ruɗe saboda su, matan kuwa suka ce, “Na’omi ce wannan kuwa?”
and the two of them go until their coming to Beth-Lehem; and it comes to pass at their coming to Beth-Lehem, that all the city is moved at them, and they say, “Is this Naomi?”
20 Ta ce musu, “Kada ku kira ni Na’omi. Ku kira ni Mara gama Maɗaukaki ya sa raina ya yi ɗaci sosai.
And she says to them, “Do not call me Naomi; call me Mara, for the Almighty has dealt very bitterly to me,
21 In tafi cikakke, amma Ubangiji ya dawo da ni ba kome. Don me kuke kirana Na’omi? Ubangiji ya wahalshe ni, Maɗaukaki ya kawo mini masifa.”
I went out full, and YHWH has brought me back empty, why do you call me Naomi, and YHWH has testified against me, and the Almighty has done evil to me?”
22 Na’omi fa ta koma daga Mowab tare da Rut mutuniyar Mowab, surukarta, suka kai Betlehem a lokacin da ake fara girbin sha’ir.
And Naomi turns back, and Ruth the Moabitess, her daughter-in-law, with her, who has turned back from the fields of Moab, and they have come to Beth-Lehem at the commencement of barley-harvest.

< Rut 1 >