< Romawa 6 >

1 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba da yin zunubi domin alheri yă haɓaka?
Nipele, sambano tujileje uli? Ana tujendelechele kusigala mu sambi kuti umbone wa Akunnungu upunde?
2 Sam, ko kaɗan! Mun mutu ga zunubi; ta yaya za mu ci gaba da rayuwa a cikinsa kuma?
Ngwamba! Patukusala nkati machili ga sambi syasili mwetuwe, uweji tuli mpela ŵatuwile, ana tutukombole uli kutama sooni mu sambi?
3 Ko ba ku sani ba cewa dukanmu da aka yi wa baftisma a cikin Kiristi Yesu an yi mana baftismar ne zuwa cikin mutuwarsa?
Pakuŵa nkumanyilila kuti twabatiswe nkulumbikana ni Kilisito Che Yesu, ni kwa litala lya ubatiso twalumbikene nawo mu chiwa chao.
4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka tā da Kiristi daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa.
Patwabatisilwe twalumbikene ni chiwa chao ni kusikwa pamo nawo, kuti mpela iŵatite pakusyuswa Kilisito mu ŵawe kwa litala lya ukulu wa Atati, iyoyo peyo noweji tukombole kutama mu umi wa sambano.
5 In kuwa mun zama ɗaya tare da shi haka a cikin mutuwarsa, tabbatacce mu ma za mu zama ɗaya tare da shi cikin tashinsa daga matattu.
Pakuŵa iŵaga uweji twalumbikene ni Kilisito kwa chiwa chao, iyoyo peyo tutulumbikane nawo kwa kusyuswa mpela ŵelewo.
6 Gama mun san cewa an gicciye halayenmu na dā tare da shi domin a kawar da jikin nan mai zunubi don kada mu ƙara zama bayi ga zunubi
Tukumanyilila kuti wende wetu wa kalakala waŵambikwe pa nsalaba pamo ni Kilisito kuti chiilu cha sambi chijonasiche, tukasitumichila sooni sambi.
7 domin duk wanda ya mutu an’yantar da shi daga zunubi ke nan.
Pakuŵa mundu jwawile ngakuŵa sooni paasi pa machili ga sambi syasikupanganya masengo nkati mwao.
8 To, in mun mutu tare da Kiristi, mun gaskata cewa za mu rayu tare da shi kuma.
Nambo iŵaga tuwile pamo ni Kilisito, tukukulupilila kuti chitutame pamo nawo.
9 Gama mun san cewa da yake an tā da Kiristi daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba; mutuwa ba ta da sauran iko a kansa.
Pakuŵa tukumanyilila kuti Kilisito asyuchile, nombewo ngaawa sooni, pakuŵa chiwa ngachatawala sooni.
10 Mutuwar da ya yi, ya mutu ne sau ɗaya tak, saboda yă shafe zunubi, amma rayuwar da yake yi, yana yi ne cikin tarayya da Allah.
Pakuŵa ŵawile kamo pe kwa ligongo lya sambi, ngaawa sooni, nambo kwakutama kwakwe, sambano akutama nkulumbikana ni Akunnungu.
11 Haka ku ma, ku ɗauke kanku matattu ne ga ikon zunubi amma rayayyu cikin tarayya da Allah cikin Kiristi Yesu.
Iyoyo peyo ni ŵanyamwe nombe nliŵalanje ŵawe nkati ngani ja machili ga sambi ni kutama pamo ni Akunnungu nkulumbikana ni Kilisito Yesu.
12 Saboda haka kada ku bar zunubi yă mallaki jikin nan naku mai mutuwa yă sa ku zama masu biyayya ga mugayen sha’awace-sha’awacensa.
Nipele, nkasileka sooni sambi sitawale mu iilu yenu ya kuwa, kuti nkasijitichisya tama sya pachiilu.
13 Kada ku miƙa gaɓoɓin jikinku ga zunubi a matsayin kayan aikin mugunta, sai dai ku miƙa kanku ga Allah, a matsayin waɗanda aka fitar da su daga mutuwa zuwa rai; ku kuma miƙa gaɓoɓin jikinku gare shi a matsayin kayan aikin adalci.
Kasinyikoposya iŵalo yenu nachiŵamuno chimo kwa ligongo lya kutenda sambi. Nambo nlityosye mwachinsyene kwa Akunnungu nti ŵandu ŵasyuswe, ni nnyityosye iŵalo yenu itumiche kwa kupanganya yambone paujo pa Akunnungu.
14 Gama zunubi ba zai zama maigidanku ba, domin ba kwa ƙarƙashin doka, sai dai ƙarƙashin alheri.
Sambi sinantawale sooni, ligongo nganimma paasi pa malajisyo nambo nkulongoswa ni ntuuka wa Akunnungu.
15 Me za mu ce ke nan? Za mu ci gaba yin zunubi domin ba ma ƙarƙashin doka sai dai ƙarƙashin alheri? Sam, ko kaɗan!
Nipele, tujileje uli? Ana tujendelechele kutenda sambi pakuŵa nganituŵa paasi pa malajisyo, nambo tukulongoswa ni ntuuka wa umbone wa Akunnungu? Ngwamba!
16 Ba ku sani ba cewa sa’ad da kuka miƙa kanku ga wani don ku yi masa biyayya a matsayin bayi, ko ku bayi ne ga zunubi, wanda yake kai ga mutuwa, ko kuwa ga biyayya, wadda take kai ga adalci, ashe, ba kun zama bayi ga wannan da kuke yi wa biyayya ba ke nan?
Nkumanyililanga kuti mwalityosyaga mwachinsyene mpela achikapolo kwa kunjitichisya mundu jwine, isyene nkuŵa achikapolo ŵa mundu jo. Mwaŵaga achikapolo ŵa sambi, mbesi jakwe chiwa ni mwaŵaga achikapolo ŵa kwajitichisya Akunnungu, mbesi jakwe nkutendekwa kuŵa ŵambone paujo pao.
17 Amma godiya ga Allah don ko da yake a dā ku bayi ne ga ikon zunubi, da dukan zuciyarku kun yi biyayya ga irin koyarwar da aka danƙa muku.
Nambo ngwatogolela Akunnungu, namose mwaliji achikapolo ŵa sambi kalakala ko, nambo sambano mpochele kwa ntima wose usyene wauli mmajiganyo gimpochele.
18 An’yanta ku daga zunubi, kun kuma zama bayi ga aikin adalci.
Mmombochekwe kutyochela mu ukapolo wa sambi, ni sambano mmele achikapolo ŵakupanganya yaili yambone paujo pa Akunnungu.
19 Ina magana ne kamar mutane saboda kun raunana a jikinku. Kamar yadda kuka saba miƙa gaɓoɓin jikinku a bautar abubuwan ƙazanta da mugun aiki a kan mugun aiki, saboda haka yanzu sai ku miƙa su bayi ga aikin adalci mai kai ga zaman tsarki.
Nguŵecheta kwa maloŵe ga moŵa gose pakuŵa ngankukombola kumanyilila. Pakuŵa kalakala ko mwalityosisye iilu yenu mme achikapolo ŵa usakwa ni ugongomalo. Iyoyo peyo sambano nlityosye mwachinsyene mme achikapolo ŵakupanganya yambone paujo pa Akunnungu kuti nkombole kuswejeswa.
20 Sa’ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci.
Pamwalinji achikapolo ŵa sambi, nganintaŵikwa kupanganya indu yambone paujo pa Akunnungu.
21 Wace riba ce kuka samu a lokacin, daga abubuwan nan da yanzu suka zama muku abin kunya? Ƙarshen irin abubuwan nan dai, mutuwa ne!
Ana mwapochile chichi pa moŵa go pamwapangenye indu yankuiwona kuti ili indu ya soni sambano jino? Pakuŵa kumbesi kwa indu yo kuli chiwa.
22 Amma a yanzu da aka’yantar da ku daga zunubi kuka kuma zama bayi ga Allah, ribar da kuka samu tana kai ga zaman tsarki, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. (aiōnios g166)
Nambo sambano mmasile kuwombolwa mu ukapolo wa sambi ni kutendekwa achikapolo ŵa Akunnungu. Chinkupoka sambano chili kutama mu kuswejeswa kwakukwikanawo umi wa moŵa gose pangali mbesi. (aiōnios g166)
23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma kyautar Allah rai madawwami ne a cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu. (aiōnios g166)
Pakuŵa mbote ja sambi jili chiwa nambo ntuuka waakukoposya Akunnungu uli umi wa moŵa gose pangali mbesi mu kulumbikana ni Kilisito Yesu Ambuje ŵetu. (aiōnios g166)

< Romawa 6 >