< Ru’uya ta Yohanna 5 >

1 Sa’an nan na ga a hannun damar wannan wanda yake zaune a kursiyin naɗaɗɗen littafi da rubutu a ciki da wajensa an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
Und ich sah in der Rechten Dessen, Der auf dem Throne saß, ein Buch, inwendig und auswendig beschrieben, versiegelt mit sieben Siegeln.
2 Na kuma ga wani babban mala’ika yana shela da babbar murya cewa, “Wa ya cancanta yă ɓalle hatiman nan yă kuma buɗe naɗaɗɗen littafin?”
Und ich sah einen starken Engel mit großer Stimme ausrufen: Wer ist würdig, das Buch aufzutun und seine Siegel zu lösen?
3 Amma ba wani a sama ko a ƙasa ko a ƙarƙashin ƙasan da ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin ko ma yă duba cikinsa.
Und niemand im Himmel, noch auf Erden, noch unter der Erde konnte das Buch auftun und hineinsehen.
4 Na yi ta kuka domin ba a iya samun wanda ya cancanta yă buɗe naɗaɗɗen littafin ko yă duba cikinsa ba.
Und ich weinte sehr, daß niemand würdig gefunden wurde, das Buch aufzutun und zu lesen, noch hineinzusehen.
5 Sai ɗaya daga cikin dattawan ya ce mini, “Kada ka yi kuka! Duba, Zakin kabilar Yahuda, da kuma Tushen Dawuda ya ci nasara. Ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin da hatimansa bakwai.”
Und einer von den Ältesten sprach zu mir: Weine nicht! Siehe, der Löwe, der da ist aus dem Stamme Juda, die Wurzel Davids, hat überwunden, das Buch aufzutun und seine sieben Siegel zu lösen!
6 Sa’an nan na ga Ɗan Rago, yana kamar an yanka, tsaye a tsakiyar kursiyin, halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan an sun kewaye shi. Yana da ƙahoni bakwai da idanu bakwai, waɗanda suke ruhohi bakwai na Allah da aka aika cikin dukan duniya.
Und ich sah, und siehe, inmitten des Throns und der vier Tiere und inmitten der Ältesten stand ein Lamm, als wäre es erschlagen, das hatte sieben Hörner und sieben Augen, welche sind die sieben Geister Gottes, ausgesandt in die ganze Erde.
7 Ya zo ya karɓi naɗaɗɗen littafin daga hannun dama na wannan wanda yake zaune a kursiyin.
Und es kam und nahm das Buch aus der Rechten Dessen, Der auf dem Throne saß.
8 Bayan ya karɓa, sai halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi ƙasa a gaban Ɗan Ragon. Kowannensu yana da garaya kuma suna riƙe da kaskon zinariya cike da turare, waɗanda suke addu’o’in tsarkaka.
Und da es das Buch nahm, fielen die vier Tiere und die vierundzwanzig Ältesten vor das Lamm. Sie hatten jeder Harfen und goldene Schalen voll Räucherwerks, welches sind die Gebete der Heiligen.
9 Suka rera sabuwar waƙa, “Ka cancanci ka karɓi naɗaɗɗen littafin ka kuma buɗe hatimansa, domin an kashe ka, da jininka kuma ka sayi mutane wa Allah, daga kowace kabila da harshe da mutane da kuma al’umma.
Und singen ein neues Lied und sagen: Du bist würdig, das Buch zu nehmen und seine Siegel aufzutun; denn du wardst erschlagen und hast uns für Gott erkauft mit Deinem Blute aus allerlei Stamm und Zunge und Volk und Völkerschaft.
10 Ka mai da su masarauta da kuma firistoci, don su yi wa Allahnmu hidima, kuma za su yi mulki a duniya.”
Und uns unsrem Gotte zu Königen und Priestern gemacht, und regieren werden wir auf Erden.
11 Sai na duba na kuma ji muryar mala’iku masu yawa, yawansu kuwa ya kai dubu dubbai, da kuma dubu goma sau dubu goma. Suka kewaye kursiyin da halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan.
Und ich sah, und hörte die Stimme vieler Engel rings um den Thron und die Tiere und die Ältesten, und ihre Zahl war Myriaden von Myriaden und Tausende von Tausenden.
12 Da babbar murya suka rera, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe, don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”
Und sie sagten mit großer Stimme: Würdig ist das Lamm, das erschlagene, zu nehmen die Kraft und Reichtum und Weisheit und Stärke und Ehre und Herrlichkeit und Segen.
13 Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn g165)
Und alles Geschaffene, das da ist im Himmel und auf Erden und unter der Erde, und die im Meere sind, und alles, was in denselben ist, hörte ich sagen: Dem, Der auf dem Throne sitzt und dem Lamme sei der Segen und die Ehre und die Herrlichkeit und die Macht in die Zeitläufe der Zeitläufe. (aiōn g165)
14 Sai halittu huɗun nan masu rai suka ce, “Amin”, dattawan kuma suka fāɗi suka yi sujada.
Und die vier Tiere sprachen: Amen! Und die vierundzwanzig Ältesten fielen nieder und beteten an Ihn, Der da lebt in die Zeitläufe der Zeitläufe.

< Ru’uya ta Yohanna 5 >