< Ru’uya ta Yohanna 17 >

1 Ɗaya daga cikin mala’iku bakwai masu ɗauke da kwanoni bakwai nan, ya zo ya ce mini, “Zo, zan nuna maka hukuncin babbar karuwan nan da take zaune a bisan ruwaye masu yawa.
And there came one of the seven angels who had the seven bowls, and spoke to me, saying, "Come hither and I will show you the sentence passed upon the great harlot who sits on many waters,
2 Da ita ce sarakunan duniya suka yi zina mazaunan duniya kuma suka bugu da ruwan inabin zinace zinacenta.”
with whom the kings of the earth have committed adultery, while all who live on the earth have been made drunken by the wine of her immorality."
3 Sa’an nan mala’ikan ya ɗauke ni cikin Ruhu zuwa hamada. A can na ga mace zaune a kan wata jan dabbar da aka rufe da sunayen saɓo tana kuma da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And he bore me away in the Spirit into the desert, and I saw a woman who sat upon a scarlet beast covered with blasphemous names. It had seven heads and ten horns.
4 Macen tana saye da tufafi masu ruwan ja da shunayya, tana ƙyalli da zinariya, duwatsu masu daraja da kuma lu’ulu’ai. Tana riƙe da kwaf na zinariya a hannunta, cike da abubuwa masu banƙyama da kuma ƙazantar zinace zinacenta.
The woman was enwrapped in purple and scarlet and was encrusted with gold and precious stones and pearls. In her hand she held a golden cup filled with abominations, even the impurities of her immorality.
5 Sunan da aka rubuta a goshinta asiri ne, Babilon mai girma mahaifiyar karuwai da kuma na abubuwa masu banƙyama na duniya.
Upon her forehead a name was written, a mystery, "BABYLON THE GREAT, THE MOTHER OF HARLOTS, AND ABOMINABLE THINGS OF THE EARTH."
6 Na ga cewa macen ta bugu da jinin tsarkaka, jinin waɗanda suka shaida Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai.
And I saw the woman drunk with the blood of the saints, and with the blood of the martyrs of Jesus, and I wondered with a great wonder.
7 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan bayyana maka asirin macen nan da dabbar da take hawa, wadda take da kawuna bakwai da ƙahoni goma.
And the angel said to me. "Why did you wonder? I will explain to you the mystery of the woman, and of the beast with the seven heads and ten horns, that carried her.
8 Dabbar da ka gani, a dā ta taɓa kasancewa, a yanzu, ba ta, za tă kuma fito daga Abis zuwa ga hallakarta. Mazaunan duniya waɗanda ba a rubuta sunayensu a littafin rai tun kafin halittar duniya ba za su yi mamaki sa’ad da suka ga dabbar, domin a dā ta taɓa kasancewa, yanzu kuwa ba ta, duk da haka za tă dawo. (Abyssos g12)
The beast that you saw was, and is not, and is about to come up out of the bottomless pit, and to go into perdition. And those who dwell on the earth shall wonder, those whose names have never, from the foundation of the world, been written in the Lamb’s Book of Life, when they gaze on the beast; how he was and is not, and is to come. (Abyssos g12)
9 “Wannan yana bukata hankali da kuma hikima. Kawuna bakwai nan tuddai bakwai ne da macen take zama a kai.
Here is the mind that has wisdom. the seven heads are seven hills on which the woman is seated;
10 Sarakuna bakwai ne kuma. Biyar sun fāɗi, ɗaya yana nan, ɗayan kuma bai zo ba tukuna; amma sa’ad da ya zo, zai kasance na ɗan lokaci.
and they are seven kings; the five have fallen, one is, the other is not yet come (and when he does come, he must remain a short time).
11 Dabbar da a dā ta taɓa kasancewa, amma yanzu ba ta, ita ce sarki na takwas. Ita ɗaya ce cikin bakwai ɗin, kuma tana tafiya zuwa ga hallakarta.
And the beast who was, but is not, is himself also an eighth, although he is one of the seven kings, and is on his way to perdition.
12 “Ƙahonin nan goma da ka gani sarakuna goma ne da ba su riga sun karɓi mulki ba, amma waɗanda na sa’a guda za su karɓi iko a matsayin sarakuna tare da dabbar.
"The ten horns that you saw are ten kings who have not yet received their kingdoms; but they have received authority as kings for one hour, together with the beast.
13 Suna da manufa guda za su kuma ba wa dabbar ikonsu da kuma sarautarsu.
These kings have one mind, and they give their power and authority to the beast.
14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, sai dai Ɗan Ragon zai ci nasara a bisansu domin shi ne Ubangijin iyayengiji, Sarkin sarakuna, tare da shi kuwa kirayayunsa, zaɓaɓɓunsa da kuma amintattu masu binsa za su kasance.”
These will make war against the Lamb, and the Lamb will conquer them, for he is the Lord of lords, and King of kings. And they who are with him are called and faithful and chosen."
15 Sa’an nan mala’ikan ya ce mini, “Ruwayen da ka gani, inda karuwan take zama, jama’a ce, taro masu yawa, al’ummai da kuma harsuna.
And he also said to me. "The waters which you saw, on which the harlot takes her seat, are peoples and multitudes and nations and tongues.
16 Dabbar da kuma ƙahoni goma da ka gani za su ƙi jinin karuwar. Za su kai ta ga hallaka su kuma bar ta tsirara; za su ci namanta su kuma ƙone ta da wuta.
And the ten horns which you saw, they and the beast will hate the harlot and make her desolate and naked, and will eat her flesh and burn her up with fire.
17 Gama Allah ya sa a zukatansu su cika nufinsa ta wurin yarda su ba wa dabbar ikonsu tă yi mulki, sai lokacin da kalmomin Allah sun cika.
For God has put it into their hearts to execute his purpose, in executing their common purpose, and by giving over their kingdoms to the beast, until the words of God shall be accomplished.
18 Macen da ka gani ita ce babban birnin da yake mulki a bisan sarakunan duniya.”
The woman whom you saw is the great city which holds sway over the kings of the earth."

< Ru’uya ta Yohanna 17 >