< Zabura 99 >

1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
Yahweh is the [supreme] king, so [all] the people-groups should tremble ([in his presence/in front of him])! He sits on his throne [in the temple] above the [statues of] winged creatures, [so] the earth should quake/shake!
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
Yahweh is a mighty [king] in Jerusalem; [but] he is [also] the supreme ruler of all people-groups.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
[So] they should praise him because he is very great/powerful; and he is holy!
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
He is a mighty king who (loves/is pleased with) what is just/right; he has acted justly and fairly [DOU] in Israel.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Praise Yahweh our God! Worship him [in front of the Sacred Chest in his temple] [MTY], where he rules people. He is holy!
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Moses and Aaron were two of his priests; Samuel also was someone who prayed to him. Those [three] cried out to Yahweh [to help them], and he answered them.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
He spoke to Moses and Aaron from the cloud [that was like a huge] pillar; they obeyed [all] the laws and commandments [DOU] that he gave to them.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Yahweh, our God, you answered [your people] [when they cried out to you to help them]; you are a God who forgave them [for those sins that they had committed], even though you punished them for the things that they did that are wrong.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Praise Yahweh, our God, and worship him [at the temple] on his sacred hill; [it is right to do that] because Yahweh, our God, is holy!

< Zabura 99 >