< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Cantad a Yahvé un cántico nuevo, cantad a Yahvé, tierras todas.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Cantad a Yahvé, bendecid su nombre, proclamad día tras día su salvación.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Pregonad su gloria entre los gentiles; sus maravillas entre los pueblos todos.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande es Yahvé y digno de suma alabanza, temible, más que todos los dioses.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
Pues todos los dioses de los gentiles son ficción en tanto que Yahvé hizo los cielos.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Majestad y belleza le preceden; en su santa morada están el poder y la gloria.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Reconoced a Yahvé, oh razas de los pueblos, reconoced a Yahvé la gloria y el poder.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Reconoced a Yahvé la gloria de su Nombre. Traedle oblaciones y venid a sus atrios.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Adorad a Yahvé en sacro esplendor, oh tierra toda, tiembla ante ÉL
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Anunciad a las naciones: “Reina Yahvé; Él ha dado estabilidad al orbe, para que no vacile; rige a los pueblos con justicia.”
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Alégrense los cielos, y regocíjese la tierra; retumbe el mar y cuanto lo llena;
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
salte de júbilo el campo con todo lo que hay en él. Rebosarán entonces de exultación todos los árboles de la selva,
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
ante la presencia de Yahvé, porque viene, porque viene para gobernar la tierra. Gobernará la redondez de la tierra con justicia, y a los pueblos con su fidelidad.

< Zabura 96 >