< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Kommet, laßt uns Jehovah lobpreisen, lasset uns aufjauchzen dem Felsen unseres Heils.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Laßt uns mit Bekennen vor Sein Angesicht kommen, laßt uns Ihm aufjauchzen mit Psalmen.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Denn ein großer Gott ist Jehovah, und ein großer König über alle Götter.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
In Dessen Hand sind der Erde Ergründungen, und Dessen sind der Berge Kräfte.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Dessen ist das Meer und Er hat es gemacht, und das Trockene, das Seine Hände bildeten.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Kommt, laßt uns anbeten und uns beugen und knien vor Jehovah, Der uns gemacht.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Denn Er ist unser Gott und wir sind Seiner Weide Volk, und die Schafe Seiner Hand, diesen Tag, wenn ihr auf Seine Stimme hört,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Verhärtet nicht euer Herz, wie in Meribah, wie am Tage Massahs in der Wüste;
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Wo eure Väter Mich versuchten, Mich prüften, auch Mein Werk sahen.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Vierzig Jahre hatte Ich Verdruß an dem Geschlecht, und Ich sprach: Es ist ein Volk, das irren Herzens ist, und sie erkennen Meine Wege nicht.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Denen Ich in Meinem Zorn schwur: Sie sollen nicht eingehen zu Meiner Ruhe.

< Zabura 95 >