< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Ya RAB, öç alıcı Tanrı, Saç ışığını, ey öç alıcı Tanrı!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Kalk, ey yeryüzünün yargıcı, Küstahlara hak ettikleri cezayı ver!
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Kötüler ne zamana dek, ya RAB, Ne zamana dek sevinip coşacak?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Ağızlarından küstahlık dökülüyor, Suç işleyen herkes övünüyor.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Halkını eziyorlar, ya RAB, Kendi halkına eziyet ediyorlar.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Dulu, garibi boğazlıyor, Öksüzleri öldürüyorlar.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
“RAB görmez” diyorlar, “Yakup'un Tanrısı dikkat etmez.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Ey halkın içindeki budalalar, dikkat edin; Ey aptallar, ne zaman akıllanacaksınız?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Kulağı yaratan işitmez mi? Göze biçim veren görmez mi?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Ulusları yola getiren yargılamaz mı? İnsanı eğiten bilmez mi?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
RAB insanın düşüncelerinin Boş olduğunu bilir.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Ne mutlu, ya RAB, yola getirdiğin, Yasanı öğrettiğin insana!
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Kötüler için çukur kazılıncaya dek, Onu sıkıntılı günlerden kurtarıp rahatlatırsın.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Çünkü RAB halkını reddetmez, Kendi halkını terk etmez.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Adalet yine doğruluk üzerine kurulacak, Yüreği temiz olan herkes ona uyacak.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Kötülere karşı beni kim savunacak? Kim benim için suçlulara karşı duracak?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
RAB yardımcım olmasaydı, Şimdiye dek sessizlik diyarına göçmüştüm bile.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
“Ayağım kayıyor” dediğimde, Sevgin ayakta tutar beni, ya RAB.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Kaygılar içimi sarınca, Senin avutmaların gönlümü sevindirir.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Yasaya dayanarak haksızlık yapan koltuk sahibi Seninle bağdaşır mı?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Onlar doğruya karşı birleşiyor, Suçsuzu ölüme mahkûm ediyorlar.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Ama RAB bana kale oldu, Tanrım sığındığım kaya oldu.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Tanrımız RAB yaptıkları kötülüğü Kendi başlarına getirecek, Kötülükleri yüzünden köklerini kurutacak, Evet, köklerini kurutacak.

< Zabura 94 >