< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O LORD, Thou God to whom vengeance belongeth, Thou God to whom vengeance belongeth, shine forth.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Lift up Thyself, Thou Judge of the earth; render to the proud their recompense.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
LORD, how long shall the wicked, how long shall the wicked exult?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
They gush out, they speak arrogancy; all the workers of iniquity bear themselves loftily.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
They crush Thy people, O LORD, and afflict Thy heritage.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They slay the widow and the stranger, and murder the fatherless.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
And they say: 'The LORD will not see, neither will the God of Jacob give heed.'
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Consider, ye brutish among the people; and ye fools, when will ye understand?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He that planted the ear, shall He not hear? He that formed the eye, shall He not see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He that instructeth nations, shall not He correct? even He that teacheth man knowledge?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The LORD knoweth the thoughts of man, that they are vanity.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Happy is the man whom Thou instructest, O LORD, and teachest out of Thy law;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
That Thou mayest give him rest from the days of evil, until the pit be digged for the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For the LORD will not cast off His people, neither will He forsake His inheritance.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
For right shall return unto justice, and all the upright in heart shall follow it.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will rise up for me against the evil-doers? Who will stand up for me against the workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Unless the LORD had been my help, my soul had soon dwelt in silence.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I say: 'My foot slippeth', Thy mercy, O LORD, holdeth me up.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
When my cares are many within me, Thy comforts delight my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Shall the seat of wickedness have fellowship with Thee, which frameth mischief by statute?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They gather themselves together against the soul of the righteous, and condemn innocent blood.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the LORD hath been my high tower, and my God the rock of my refuge.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And He hath brought upon them their own iniquity, and will cut them off in their own evil; the LORD our God will cut them off.

< Zabura 94 >