< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O Lord God the auenger, O God the auenger, shewe thy selfe clearely.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Exalt thy selfe, O Iudge of the worlde, and render a reward to the proude.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Lord how long shall the wicked, how long shall the wicked triumph?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
They prate and speake fiercely: all the workers of iniquitie vaunt themselues.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
They smite downe thy people, O Lord, and trouble thine heritage.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They slay the widowe and the stranger, and murder the fatherlesse.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Yet they say, The Lord shall not see: neither will the God of Iaakob regard it.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Vnderstande ye vnwise among the people: and ye fooles, when will ye be wise?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Hee that planted the eare, shall hee not heare? or he that formed the eye, shall he not see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Or he that chastiseth the nations, shall he not correct? hee that teacheth man knowledge, shall he not knowe?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The Lord knoweth the thoughtes of man, that they are vanitie.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Blessed is the man, whom thou chastisest, O Lord, and teachest him in thy Lawe,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
That thou mayest giue him rest from the dayes of euill, whiles the pitte is digged for the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Surely the Lord will not faile his people, neither will he forsake his inheritance.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
For iudgement shall returne to iustice, and all the vpright in heart shall follow after it.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will rise vp with me against the wicked? or who will take my part against the workers of iniquitie?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
If the Lord had not holpen me, my soule had almost dwelt in silence.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
When I said, My foote slideth, thy mercy, O Lord, stayed me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
In the multitude of my thoughts in mine heart, thy comfortes haue reioyced my soule.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Hath the throne of iniquitie fellowship with thee, which forgeth wrong for a Lawe?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They gather them together against the soule of the righteous, and condemne the innocent blood.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the Lord is my refuge, and my God is the rocke of mine hope.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And hee will recompence them their wickednes, and destroy them in their owne malice: yea, the Lord our God shall destroy them.

< Zabura 94 >