< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Es bueno alabar al Señor y hacer melodía a tu nombre, ¡oh Altísimo!
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
Para declarar tu misericordia en la mañana, y tu fe inmutable todas las noches;
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
En un instrumento de diez cuerdas, y música de arpa.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Porque tú, oh Jehová, me has agradado por tus obras; Tendré alegría en la obra de tus manos.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
¡Oh Señor, qué grandes son tus obras! y tus pensamientos son muy profundos.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
Un hombre sin sentido no tiene conocimiento de esto; y un hombre necio no puede asimilarlo.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Cuando los pecadores se levantan como la hierba, y todos los que hacen mal florecen, es para que su fin sea la destrucción eterna.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Pero tú, oh Señor, estás en lo alto para siempre.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Para ver! tus enemigos, oh Señor, morirán; todos los hacedores del mal serán esparcidos;
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Pero mi fuerzas aumentan como las del búfalo; el mejor aceite fluye sobre mi cabeza.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mis ojos han visto problemas en mis enemigos; mis oídos tienen noticias del destino de los malhechores que se han enfrentado a mí.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
El hombre bueno será como un árbol alto en su fuerza; su crecimiento será como los árboles que se extienden en el Líbano.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Los plantados en la casa del Señor subirán altos y fuertes en sus jardines.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Darán fruto aun cuando sean viejos; serán fértiles y llenos de crecimiento;
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Para anunciar que el Señor es recto; él es mi Roca, no hay engaño en él.

< Zabura 92 >