< Zabura 92 >
1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A psalm. A song for the Sabbath day. How good it is to thank the Lord, to sing praises to you, Most High,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
to tell of your trustworthy love in the morning, and your faithfulness in the night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
to the music of a ten-stringed harp and the melody of a lyre.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
You've made me so happy, Lord, because of all you've done for me! I sing for joy at what you've done!
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Lord, what you do is amazing; your thoughts are very profound!
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
Only senseless people and fools don't know and understand this:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
even though the wicked grow up quickly like grass, and even though people who do evil flourish, they will be destroyed forever!
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But you, Lord, rule on high forever.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Your enemies, Lord, your enemies will die; everyone who does evil will be destroyed!
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But you have made me as powerful as a wild bull; you have anointed me with the best olive oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
My eyes look with pleasure to see my enemies defeated; my ears have heard the downfall of those who tried to attack me.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Those who live right flourish like a palm tree; they grow tall like a cedar tree in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
They are planted in the house of the Lord; they thrive in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Even when they are old they will still produce fruit, staying fresh and green.
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
They will declare, “The Lord does what is right! He is my rock! There is no wrong in him!”