< Zabura 9 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
“To the chief musician upon Muthlabben, a psalm of David.” I will thank the Lord with all my heart: I will relate all thy marvelous deeds.
2 Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
I will rejoice and exult in thee: I will sing praise to thy name, O thou Most High:
3 Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
When my enemies are turned backward, [when] they fall and perish at thy presence.
4 Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
For thou hast conducted my dispute and my cause; thou hast sat on the throne as a righteous judge.
5 Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
Thou hast rebuked nations, thou hast caused the wicked to perish, their name hast thou blotted out for ever and ever.
6 Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
O thou enemy, the ruins are passed away for ever, and the cities which thou hast destroyed, —lost is their memorial, yea, theirs.
7 Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
But the Lord will sit enthroned for ever: he hath established for giving judgment his throne.
8 Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
And he will judge the world with righteousness, he shall decide for the people, with equity.
9 Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
The Lord also will be a strong-hold for the oppressed, a strong-hold in times of distress.
10 Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
And they that know thy name will put their trust in thee; for thou hast not forsaken those that seek thee, O Lord.
11 Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
Sing praises to the Lord, who dwelleth in Zion: announce among the people his deeds.
12 Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
For he, that inquireth after acts of blood, hath remembered them: he hath not forgotten the cry of the afflicted.
13 Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
Be gracious unto me, O Lord; have regard to my affliction [coming] from those that hate me, thou who liftest me up from the gates of death:
14 don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
In order that I may relate all thy praises in the gates of the daughters of Zion: I will be glad in thy salvation.
15 Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
Sunk are nations in the ditch that they have prepared: in this net which they had laid in secret is their own foot caught.
16 An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
The Lord is made known: he executed justice: through the doing of his own hands is the wicked ensnared. Higgayon, (Selah)
17 Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol h7585)
The wicked shall return into hell, all the nations that are forgetful of God. (Sheol h7585)
18 Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
For not everlastingly shall the needy be forgotten: the expectation of the poor shall not perish for ever.
19 Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
Arise, O Lord; let not the mortal boast of his strength; let nations be judged before thy face.
20 Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)
Place, O Lord, fear over them: let nations know, that they are but mortals. (Selah)

< Zabura 9 >